< Nehemiya 11 >
1 To, fa, shugabannin mutane suka zauna a Urushalima, sauran mutanen kuma suka jefa ƙuri’a don su kawo mutum ɗaya daga kowane mutum goma don su zauna a Urushalima, birni mai tsarki, yayinda sauran tara suka zauna a garuruwansu.
Les princes du peuple habitaient à Jérusalem. Le reste du peuple tirait aussi au sort une part de dix pour habiter à Jérusalem, la ville sainte, et neuf parts dans les autres villes.
2 Sai mutane suka yaba wa dukan mutanen da suka ba da kansu da yardar rai su zauna a Urushalima.
Le peuple bénissait tous les hommes qui s'offraient volontairement pour habiter à Jérusalem.
3 Waɗannan su ne shugabannin yankuna waɗanda suka zauna a Urushalima (ko da yake waɗansu Isra’ilawa, da firistoci, da Lawiyawa, da ma’aikatan haikali, da zuriyar bayin Solomon, suka yi zama a cikin garuruwan Yahuda, kowanne a mallakarsa cikin garuruwa dabam-dabam,
Voici les chefs de la province qui habitaient à Jérusalem; mais dans les villes de Juda, chacun habitait dans sa propriété dans ses villes: Israël, les prêtres, les lévites, les serviteurs du temple et les enfants des serviteurs de Salomon.
4 yayinda sauran mutane daga Yahuda da Benyamin suka zauna a Urushalima). Daga zuriyar Yahuda akwai, Atahiya ɗan Uzziya, ɗan Zakariya, ɗan Amariya, ɗan Shefatiya, ɗan Mahalalel, wani zuriyar Ferez;
Une partie des fils de Juda et des fils de Benjamin habitaient à Jérusalem. Des fils de Juda: Athaja, fils d'Ozias, fils de Zacharie, fils d'Amaria, fils de Shephatia, fils de Mahalalel, des fils de Pérez;
5 da Ma’asehiya ɗan Baruk, ɗan Kol-Hoze, ɗan Hazahiya, ɗan Adahiya, ɗan Yohiyarib, ɗan Zakariya, zuriyar Shela.
Maaséja, fils de Baruch, fils de Colhozeh, fils de Hazaja, fils d'Adaja, fils de Joiarib, fils de Zacharie, fils du Shilonite.
6 Zuriyar Ferez waɗanda suka zauna a Urushalima sun kai ɗari huɗu da sittin da takwas, dukansu kuwa muhimman mutane ne.
Tous les fils de Pérez qui habitaient à Jérusalem étaient quatre cent soixante-huit hommes vaillants.
7 Daga zuriyar Benyamin akwai, Sallu ɗan Meshullam, ɗan Yowed, ɗan Fedahiya, ɗan Kolahiya, ɗan Ma’asehiya, ɗan Itiyel, ɗan Yeshahiya,
Voici les fils de Benjamin: Sallu, fils de Meshullam, fils de Jœd, fils de Pedaja, fils de Kolaja, fils de Maaséja, fils d'Ithiel, fils de Jeshaiah.
8 da mabiyansa, Gabbai da Sallai, mutum 928.
Après lui, Gabbaï et Sallaï, neuf cent vingt-huit.
9 Yowel ɗan Zikri ne babban shugabansu, Yahuda kuma ɗan Hassenuwa, ya shugabanci Yanki na Biyu na birni.
Joël, fils de Zicri, était leur surveillant; et Juda, fils de Hassenua, était le second sur la ville.
10 Daga firistoci akwai, Yedahiya ɗan Yohiyarib, da Yakin,
Parmi les sacrificateurs: Jedaja, fils de Joiarib, Jachin,
11 da Serahiya ɗan Hilkiya, ɗan Meshullam, ɗan Zadok, ɗan Merahiyot, ɗan Ahitub, mai lura da abubuwa a cikin gidan Allah,
Seraja, fils de Hilkija, fils de Meshullam, fils de Tsadok, fils de Meraioth, fils d'Ahitub, chef de la maison de Dieu,
12 tare da’yan’uwansu waɗanda suke aiki domin haikali, su 822 ne. Akwai kuma Adahiya ɗan Yeroham, ɗan Felaliya, ɗan Amzi, ɗan Zakariya, ɗan Fashhur, ɗan Malkiya,
et leurs frères qui faisaient les travaux de la maison, huit cent vingt-deux; Adaja, fils de Jerocham, fils de Pelalia, fils d'Amzi, fils de Zacharie, fils de Pashhur, fils de Malkija,
13 da’yan’uwansa waɗanda suke shugabannin iyalai, su 242. Sai kuma Amashsai ɗan Azarel, ɗan Ahzai, ɗan Meshillemot, ɗan Immer,
et ses frères, chefs de famille, deux cent quarante-deux; Amashsaï, fils d'Azarel, fils d'Ahzaï, fils de Meshillemoth, fils d'Immer,
14 da’yan’uwansa, su 128 ne muhimman mutane. Babban shugabansu shi ne Zabdiyel ɗan Haggedolim.
et leurs frères, vaillants hommes, cent vingt-huit; et leur chef était Zabdiel, fils de Haggedolim.
15 Daga Lawiyawa kuwa akwai, Shemahiya ɗan Hasshub, ɗan Azrikam, ɗan Hashabiya, ɗan Bunni,
Parmi les Lévites: Schemaeja, fils de Hasshub, fils d'Azrikam, fils de Haschabia, fils de Bunni;
16 da Shabbetai, da kuma Yozabad, biyu cikin shugabanni Lawiyawa waɗanda suke da nawayar aiki waje da gidan Allah.
Shabbethaï et Jozabad, des chefs des Lévites, qui avaient la surveillance des affaires extérieures de la maison de Dieu;
17 Sai kuma Mattaniya ɗan Mika, ɗan Zabdi, ɗan Asaf, shugaban da yake bi da hidimar godiya da kuma addu’a. Sai Bakbukiya, na biyu a cikin’yan’uwansa; da Abda ɗan Shammuwa, ɗan Galal, ɗan Yedutun.
et Mattania, fils de Mica, fils de Zabdi, fils d'Asaph, qui était le chef pour commencer les actions de grâces en prière, et Bakbukiah, le second parmi ses frères; et Abda, fils de Shammua, fils de Galal, fils de Jeduthun.
18 Lawiyawan da suke cikin birni mai tsarki sun kai 284.
Tous les Lévites de la ville sainte étaient au nombre de deux cent quatre-vingt-quatre.
19 Matsaran ƙofofi kuwa su ne, Akkub, da Talmon, da’yan’uwansu waɗanda suke tsaron ƙofofi, su 172 ne.
Les gardiens des portes, Akkub, Talmon et leurs frères, qui surveillaient les portes, étaient au nombre de cent soixante-douze.
20 Sauran Isra’ilawa tare da firistoci, da Lawiyawa sun kasance a dukan garuruwan Yahuda, kowanne a mallakar kakansa.
Le reste d'Israël, les prêtres et les lévites étaient dans toutes les villes de Juda, chacun dans son héritage.
21 Ma’aikatan haikali sun zauna a kan tudun Ofel. Ziha, da Gishfa ne suke lura da su.
Mais les serviteurs du temple habitaient à Ophel, et Ziha et Gishpa étaient à la tête des serviteurs du temple.
22 Babban shugaban Lawiyawa a Urushalima shi ne Uzzi ɗan Bani, ɗan Hashabiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mika. Uzzi yana ɗaya daga zuriyar Asaf, waɗanda suke mawaƙan da suke da nawayar hidima a gidan Allah.
Le surveillant des Lévites à Jérusalem était Uzzi, fils de Bani, fils de Haschabia, fils de Matthania, fils de Mica, d'entre les fils d'Asaph, les chantres, qui étaient chargés des affaires de la maison de Dieu.
23 Mawaƙa sun bi umarnan sarki, a kan abin da za su yi kowace rana.
Car il y avait un ordre du roi à leur sujet, et une provision fixe pour les chantres, selon les besoins de chaque jour.
24 Fetahahiya ɗan Meshezabel, ɗaya daga zuriyar Zera ɗan Yahuda ne, wakilin sarki cikin dukan al’amuran da suka shafi mutane.
Pethahia, fils de Meshezabel, des fils de Zérach, fils de Juda, était auprès du roi pour tout ce qui concernait le peuple.
25 Game da ƙauyukan da filayensu, waɗansu mutanen Yahuda suka zauna a Kiriyat Arba da ƙauyukanta, da Dibon da ƙauyukanta, da Yekabzeyel da ƙauyukanta.
Quant aux villages avec leurs champs, des fils de Juda habitèrent à Kiriath Arba et dans ses villes, à Dibon et dans ses villes, à Jekabzeel et dans ses villages,
26 Akwai su kuma a Yeshuwa, da Molada, da Bet-Felet,
à Jeshua, à Molada, à Beth Pelet,
27 da Hazar Shuwal, da Beyersheba da ƙauyukanta.
à Hazar Shual, à Beersheba et ses villes,
28 Akwai su a Ziklag, da Mekona da ƙauyukanta.
à Ziklag, à la Mecque et ses villes,
29 Suna nan kuma a En Rimmon, da Zora, da Yarmut,
à En Rimmon, à Zorah, à Jarmuth,
30 da Zanowa, da Adullam da ƙauyukansu, da Lakish da gonakinta, da kuma Azeka da ƙauyukanta. Saboda haka sun yi zama tun daga Beyersheba har zuwa Kwarin Hinnom.
à Zanoa, à Adullam et leurs villages, à Lakis et ses champs, à Azéka et ses villes. Ils campèrent ainsi depuis Beer Schéba jusqu'à la vallée de Hinnom.
31 Zuriyar mutanen Benyamin daga Geba sun zauna a Mikmash, da Aiya, da Betel da ƙauyukanta,
Les fils de Benjamin habitaient aussi depuis Guéba, à Micmasch et à Aija, à Béthel et aux villes de son ressort,
32 da Anatot, da Nob, da Ananiya,
à Anathoth, à Nob, à Anania,
33 da Hazor, da Rama, da Gittayim,
à Hatsor, à Rama, à Gittaïm,
34 da Hadid, da Zeboyim, da Neballat,
à Hadid, à Zeboïm, à Neballat,
35 da Lod, da Ono, da kuma a Kwarin Masu sana’a.
à Lod, et à Ono, la vallée des artisans.
36 Waɗansu gundumomin Lawiyawan Yahuda sun zauna a Benyamin.
Parmi les Lévites, certaines divisions de Juda s'établirent dans le territoire de Benjamin.