< Nehemiya 11 >
1 To, fa, shugabannin mutane suka zauna a Urushalima, sauran mutanen kuma suka jefa ƙuri’a don su kawo mutum ɗaya daga kowane mutum goma don su zauna a Urushalima, birni mai tsarki, yayinda sauran tara suka zauna a garuruwansu.
Koro jotend oganda nodak Jerusalem, kendo joma nodongʼ nogoyo ombulu ka giyiero achiel kuom ji apar mondo odag Jerusalem, dala maduongʼ maler, to ji ochiko mane odongʼ, to nowe e miechgi.
2 Sai mutane suka yaba wa dukan mutanen da suka ba da kansu da yardar rai su zauna a Urushalima.
Ji nogoyo erokamano ne joma nochiwore mondo odag Jerusalem.
3 Waɗannan su ne shugabannin yankuna waɗanda suka zauna a Urushalima (ko da yake waɗansu Isra’ilawa, da firistoci, da Lawiyawa, da ma’aikatan haikali, da zuriyar bayin Solomon, suka yi zama a cikin garuruwan Yahuda, kowanne a mallakarsa cikin garuruwa dabam-dabam,
Magi e jotelo mane odak Jerusalem mamoko ne gin jo-Israel, jodolo, jo-Lawi, jotij hekalu kod nyikwa jotij Solomon manodak e mier matindo mag Juda, ka moro ka moro e kare owuon e mier matindo mopogore opogore.
4 yayinda sauran mutane daga Yahuda da Benyamin suka zauna a Urushalima). Daga zuriyar Yahuda akwai, Atahiya ɗan Uzziya, ɗan Zakariya, ɗan Amariya, ɗan Shefatiya, ɗan Mahalalel, wani zuriyar Ferez;
Jo-Juda kod jo-Benjamin bende nodak Jerusalem. Koa kuom nyikwa Juda ne gin: Athaya wuod Uzia, ma wuod Zekaria, ma wuod Amaria, ma wuod Shefatia, ma wuod Mahalalel, ma nyakwar Perez;
5 da Ma’asehiya ɗan Baruk, ɗan Kol-Hoze, ɗan Hazahiya, ɗan Adahiya, ɗan Yohiyarib, ɗan Zakariya, zuriyar Shela.
kod Maseya wuod Baruk, ma wuod Kol-Hoze, ma wuod Hazaya, ma wuod Adaya, ma wuod Joyiarib, ma wuod Zekaria, ma nyakwar Shela.
6 Zuriyar Ferez waɗanda suka zauna a Urushalima sun kai ɗari huɗu da sittin da takwas, dukansu kuwa muhimman mutane ne.
Nyikwa Perez maroteke mane odak Jerusalem noromo kwan-gi noromo ji mia angʼwen gi piero auchiel gaboro.
7 Daga zuriyar Benyamin akwai, Sallu ɗan Meshullam, ɗan Yowed, ɗan Fedahiya, ɗan Kolahiya, ɗan Ma’asehiya, ɗan Itiyel, ɗan Yeshahiya,
Koa e nyikwa Benjamin ne gin: Salu wuod Meshulam, ma wuod Joed, ma wuod Pedaya, ma wuod Kolaya, ma wuod Maseya, ma wuod Ithiel, ma wuod Jeshaya,
8 da mabiyansa, Gabbai da Sallai, mutum 928.
kod jolupne, ma gin Gabai kod Salai. Giduto ne gin ji mia ochiko gi piero ariyo gaboro.
9 Yowel ɗan Zikri ne babban shugabansu, Yahuda kuma ɗan Hassenuwa, ya shugabanci Yanki na Biyu na birni.
Joel wuod Zikri ema ne jatendgi maduongʼ, to Juda wuod Hasenua norito gwengʼ mar ariyo mar dala maduongʼno.
10 Daga firistoci akwai, Yedahiya ɗan Yohiyarib, da Yakin,
Koa kuom jodolo ne gin: Jedaya wuod Joyarib; Jakin;
11 da Serahiya ɗan Hilkiya, ɗan Meshullam, ɗan Zadok, ɗan Merahiyot, ɗan Ahitub, mai lura da abubuwa a cikin gidan Allah,
Seraya wuod Hilkia, ma wuod Meshulam, ma wuod Zadok, ma wuod Merayoth, ma wuod Ahitub, mane en jatelo morito od nyasaye,
12 tare da’yan’uwansu waɗanda suke aiki domin haikali, su 822 ne. Akwai kuma Adahiya ɗan Yeroham, ɗan Felaliya, ɗan Amzi, ɗan Zakariya, ɗan Fashhur, ɗan Malkiya,
kod jotich kaachiel kodgi, mane dhi nyime kod tich mar hekalu. Giduto ne gin ji mia aboro gi piero ariyo gariyo. Ne nitiere bende Adaya wuod Jeroham, wuod Pelalia, wuod Amzi, wuod Zekaria, wuod Pashur, wuod Malkija,
13 da’yan’uwansa waɗanda suke shugabannin iyalai, su 242. Sai kuma Amashsai ɗan Azarel, ɗan Ahzai, ɗan Meshillemot, ɗan Immer,
kod jotich kaachiel kodgi, mane jotend dhoutgi. Giduto ne gin ji mia ariyo gi piero angʼwen gariyo. Joma moko ne gin, Amashsai wuod Azarel, wuod Azai, wuod Meshilemoth, wuod Imer,
14 da’yan’uwansa, su 128 ne muhimman mutane. Babban shugabansu shi ne Zabdiyel ɗan Haggedolim.
kod joma ne tiyo kanyakla kodgi, mane gin joma roteke. Giduto ne gin ji mia achiel gi piero ariyo gaboro. Jatendgi maduongʼ ne en Zabdiel wuod Hagedolim.
15 Daga Lawiyawa kuwa akwai, Shemahiya ɗan Hasshub, ɗan Azrikam, ɗan Hashabiya, ɗan Bunni,
Koa kuom jo-Lawi ne gin: Shemaya wuod Hashub, wuod Azrikam, wuod Hashabia, wuod Buni.
16 da Shabbetai, da kuma Yozabad, biyu cikin shugabanni Lawiyawa waɗanda suke da nawayar aiki waje da gidan Allah.
Jotend jo-Lawi ariyo ma tijgi en tich ma oko mar od Nyasaye ne gin, Shabethai kod Jozabad.
17 Sai kuma Mattaniya ɗan Mika, ɗan Zabdi, ɗan Asaf, shugaban da yake bi da hidimar godiya da kuma addu’a. Sai Bakbukiya, na biyu a cikin’yan’uwansa; da Abda ɗan Shammuwa, ɗan Galal, ɗan Yedutun.
Matania wuod Mika, wuod Zabdi, wuod Asaf, notelo ne dwoko erokamano ni Nyasaye kod lamo; gi Bakbukia mane jatelo mar ariyo e kind jotich kaachiel kode; kod Abda wuod Shamua, wuod Galal, wuod Jeduthun.
18 Lawiyawan da suke cikin birni mai tsarki sun kai 284.
Jo-Lawi duto mane nitiere e dala maduongʼ malerno ne romo ji mia ariyo gi piero aboro gangʼwen.
19 Matsaran ƙofofi kuwa su ne, Akkub, da Talmon, da’yan’uwansu waɗanda suke tsaron ƙofofi, su 172 ne.
Jorit dhorangeye ne gin: Akub, Talmon kod jogo mane gitiyogo kanyakla e tij rito dhorangeye ne gin ji mia achiel gi piero abiriyo gariyo.
20 Sauran Isra’ilawa tare da firistoci, da Lawiyawa sun kasance a dukan garuruwan Yahuda, kowanne a mallakar kakansa.
Jo-Israel mamoko, kaachiel gi jodolo kod jo-Lawi, ne ni e mier matindo mag Juda, ka moro ka moro odak e lop anywolane.
21 Ma’aikatan haikali sun zauna a kan tudun Ofel. Ziha, da Gishfa ne suke lura da su.
Jotij hekalu nodak e got mar Ofel, to Ziha kod Gishpa ema ne joritgi.
22 Babban shugaban Lawiyawa a Urushalima shi ne Uzzi ɗan Bani, ɗan Hashabiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mika. Uzzi yana ɗaya daga zuriyar Asaf, waɗanda suke mawaƙan da suke da nawayar hidima a gidan Allah.
Jatelo maduongʼ mar jo-Lawi man Jerusalem ne en Uzi wuod Bani, wuod Hashabia, wuod Matania, wuod Mika. Uzi ne en achiel kuom nyikwa Asaf, ma ne gin jower, nikech tich mar od Nyasaye.
23 Mawaƙa sun bi umarnan sarki, a kan abin da za su yi kowace rana.
Jower nenie bwo chik mar ruoth, ma ema ne tijgi mapile.
24 Fetahahiya ɗan Meshezabel, ɗaya daga zuriyar Zera ɗan Yahuda ne, wakilin sarki cikin dukan al’amuran da suka shafi mutane.
Pethahia wuod Meshezabel, ma en achiel kuom nyikwa Zera wuod Juda, ne en jaote ruoth e weche duto monego ji ongʼe.
25 Game da ƙauyukan da filayensu, waɗansu mutanen Yahuda suka zauna a Kiriyat Arba da ƙauyukanta, da Dibon da ƙauyukanta, da Yekabzeyel da ƙauyukanta.
To mier mamoko kod gwenge mane jo-Juda odakie ne gin Kiriath Arba kod gwenge mokiewo kodgi, Dibon kod gwenge mokiewo kodgi, Jekabzil kod mier mokiewo kode,
26 Akwai su kuma a Yeshuwa, da Molada, da Bet-Felet,
moko nodak Jeshua, Molada, Beth Pelet,
27 da Hazar Shuwal, da Beyersheba da ƙauyukanta.
Hazar Shual, Bersheba kod gwenge mokiewo kode,
28 Akwai su a Ziklag, da Mekona da ƙauyukanta.
Ziklag, Mekona kod gwenge mokiewo kode,
29 Suna nan kuma a En Rimmon, da Zora, da Yarmut,
En Rimon, Zora, Jarmuth,
30 da Zanowa, da Adullam da ƙauyukansu, da Lakish da gonakinta, da kuma Azeka da ƙauyukanta. Saboda haka sun yi zama tun daga Beyersheba har zuwa Kwarin Hinnom.
Zanoa, Adulam kod miechgi, Lakish kod puothegi, bende joma moko nodak Azeka kod gwenge mokiewo kode. Omiyo negidak kochakore Bersheba nyaka e Holo mar Hinom.
31 Zuriyar mutanen Benyamin daga Geba sun zauna a Mikmash, da Aiya, da Betel da ƙauyukanta,
Nyikwa Benjamin mane oa Geba nodak Mikmash, Aija, Bethel kod gwenge mokiewo kodgi,
32 da Anatot, da Nob, da Ananiya,
Anathoth, Nob kod Anania,
33 da Hazor, da Rama, da Gittayim,
Hazor, Rama kod Gitaim,
34 da Hadid, da Zeboyim, da Neballat,
Hadid, Zeboim kod Nebalat,
35 da Lod, da Ono, da kuma a Kwarin Masu sana’a.
Lod gi Ono, kod e Holo mar Jopecho.
36 Waɗansu gundumomin Lawiyawan Yahuda sun zauna a Benyamin.
Jo-Lawi mamoko mane ni Juda nopog mondo odag e piny Benjamin.