< Nehemiya 10 >
1 Waɗanda suka buga hatimin su ne, Nehemiya ɗan Hakaliya, wanda yake gwamna. Zedekiya
Приложившие печати были: Неемия-Тиршафа, сын Гахалии, и Седекия,
2 da Serahiya, da Azariya, da Irmiya,
Сераия, Азария, Иеремия,
3 da Fashhur, da Amariya, da Malkiya,
Пашхур, Амария, Малхия,
4 da Hattush, da Shebaniya, da Malluk,
Хаттуш, Шевания, Маллух,
5 da Harim, da Meremot, da Obadiya,
Харим, Меремоф, Овадия,
6 da Daniyel, da Ginneton, da Baruk,
Даниил, Гиннефон, Варух,
7 da Meshullam, da Abiya, da Miyamin,
Мешуллам, Авия, Миямин,
8 da Ma’aziya, da Bilgai, da kuma Shemahiya. Waɗannan su ne Firistocin.
Маазия, Вилгай, Шемаия: это священники.
9 Lawiyawan kuwa su ne, Yeshuwa ɗan Azaniya, da Binnuyi ɗan Henadad, da Kadmiyel,
Левиты: Иисус, сын Азании, Биннуй, из сыновей Хенадада, Кадмиил,
10 ’yan’uwansu kuwa su ne, Shebaniya, da Hodiya, da Kelita, da Felahiya, da Hanan,
и братья их: Шевания, Годия, Клита, Фелаия, Ханан,
11 da Mika, da Rehob, da Hashabiya,
Миха, Рехов, Хашавия,
12 da Zakkur, da Sherebiya, da Shebaniya,
Закхур, Шеревия, Шевания,
13 da Hodiya, da Bani da kuma Beninu.
Годия, Ваний, Венинуй.
14 Shugabannin mutane su ne, Farosh, da Fahat-Mowab, da Elam, da Zattu, da Bani,
Главы народа: Парош, Пахаф-Моав, Елам, Заффу, Вания,
15 da Bunni, da Azgad, da Bebai,
Вунний, Азгар, Бевай,
16 da Adoniya, da Bigwai, da Adin,
Адония, Бигвай, Адин,
17 da Ater, da Hezekiya, da Azzur,
Атер, Езекия, Азур,
18 da Hodiya, da Hashum, da Bezai,
Годия, Хашум, Бецай,
19 da Harif, da Anatot, da Nebai,
Хариф, Анафоф, Невай,
20 da Magfiyash, da Meshullam, da Hezir,
Магпиаш, Мешуллам, Хезир,
21 da Meshezabel, da Zadok, da Yadduwa
Мешезавел, Садок, Иаддуй,
22 da Felatiya, da Hanan, da Anahiya,
Фелатия, Ханан, Анаия,
23 da Hosheya, da Hananiya, da Hasshub,
Осия, Ханания, Хашшув,
24 da Hallohesh, da Filha, da Shobek,
Лохеш, Пилха, Шовек,
25 da Rehum, da Hashabna, da Ma’asehiya
Рехум, Хашавна, Маасея,
26 da Ahiya, da Hanan, da Anan,
Ахия, Ханан, Анан,
27 da Malluk, da Harim da kuma Ba’ana.
Маллух, Харим, Ваана.
28 “Sauran mutane, wato, firistoci, Lawiyawa, matsaran ƙofofi, mawaƙa, ma’aikatan haikali da dukan waɗanda suka ware kansu daga maƙwabta saboda Dokar Allah, tare da matansu da dukan’ya’yansu maza da mata waɗanda za su iya fahimta,
И прочий народ, священники, левиты, привратники, певцы, нефинеи и все, отделившиеся от народов иноземных к закону Божию, жены их, сыновья их и дочери их, все, которые могли понимать,
29 dukan waɗannan yanzu suka sadu da manyan gari’yan’uwansu, suka rantse, cewa la’ana ta same su idan ba su kiyaye Dokar Allah da aka bayar ta wurin Musa bawan Allah su kuma mai da hankali ga yin biyayya da dukan umarnai, ƙa’idodi da farillan Ubangiji shugabanmu ba.
пристали к братьям своим, к почетнейшим из них, и вступили в обязательство с клятвою и проклятием - поступать по закону Божию, который дан рукою Моисея, раба Божия, и соблюдать и исполнять все заповеди Господа Бога нашего, и уставы Его и предписания Его,
30 “Mun yi alkawari ba za mu ba da’ya’yanmu mata aure ga mutanen da suke kewaye da mu ba, ba kuwa za mu auri’ya’yansu mata wa’ya’yanmu maza ba.
и не отдавать дочерей своих иноземным народам, и их дочерей не брать за сыновей своих;
31 “Sa’ad da maƙwabta suka kawo kayayyaki ko hatsi don su sayar a ranar Asabbaci, ba za mu saya daga gare su a ranar Asabbaci ko a rana mai tsarki ba. Kowace shekarar Asabbaci ba za mu nome ƙasa ba kuma za mu yafe kowane irin bashi.
и когда иноземные народы будут привозить товары и все продажное в субботу, не брать у них в субботу и в священный день, и в седьмой год оставлять долги всякого рода.
32 “Mun ɗauka hakkin bin umarnai na ba da kashi ɗaya bisa uku na shekel kowace shekara don hidimar gidan Allahnmu.
И поставили мы себе в закон давать от себя по трети сикля в год на потребности для дома Бога нашего:
33 Za mu tanada burodin da ake ajiye a kan tebur; za mu ba da hadayun hatsi da hadayun ƙonawa na kullum; za mu ba da hadayun Asabbatai, da na bukukkuwan Sabon Wata da na bukukkuwan da aka ƙayyade; za mu ba da hadayu masu tsarki; za mu ba da hadayun zunubi don a yi kafara domin Isra’ila; mu kuma ba da abubuwan da ake bukata dukan domin ayyukan gidan Allahnmu.
на хлебы предложения, на всегдашнее хлебное приношение и на всегдашнее всесожжение, на субботы, на новомесячия, на праздники, на священные вещи на жертвы за грех для очищения Израиля, и на все, совершаемое в доме Бога нашего.
34 “Mu, firistoci, da Lawiyawa da kuma mutane, mun jefa ƙuri’a don a san lokacin da kowane iyalinmu zai kawo sadakar itace don ƙonewa a gidan Allahnmu a ƙayyadaddun lokuta a bagaden Ubangiji Allahnmu, kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka.
И бросили мы жребии о доставке дров, священники, левиты и народ, когда которому поколению нашему в назначенные времена, из года в год, привозить их к дому Бога нашего, чтоб они горели на жертвеннике Господа Бога нашего, по написанному в законе.
35 “Mun kuma ɗauka hakkin kawo nunan fari na hatsinmu da kuma na kowane itace mai ba da’ya’ya a gidan Ubangiji kowace shekara.
И обязались мы каждый год приносить в дом Господень начатки с земли нашей и начатки всяких плодов со всякого дерева;
36 “Kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka, za mu kawo ɗan fari na’ya’yanmu maza da na garken shanunmu, da na tumakinmu, da kuma na awakinmu a gidan Allahnmu, don firistocin da suke aikin a can.
также приводить в дом Бога нашего к священникам, служащим в доме Бога нашего, первенцев из сыновей наших и из скота нашего, как написано в законе, и первородное от крупного и мелкого скота нашего.
37 “Ban da haka ma, za mu kawo wa ɗakunan ajiyar gidan Allahnmu, abincinmu na farko daga ƙasa, na hadayun hatsinmu, na’ya’yan dukan itatuwanmu da kuma na sabon ruwan inabinmu da mai namu wa firistoci. Za mu kuma kawo zakkar hatsinmu wa Lawiyawa, gama Lawiyawa ne ke karɓan Zakka cikin dukan garuruwan da muke noma.
И начатки из молотого хлеба нашего и приношений наших, и плодов со всякого дерева, вина и масла мы будем доставлять священникам в кладовые при доме Бога нашего и десятину с земли нашей левитам. Они, левиты, будут брать десятину во всех городах, где у нас земледелие.
38 Firist wanda yake daga zuriyar Haruna zai raka Lawiyawa sa’ad da suke karɓan zakka, Lawiyawan kuma za su kawo kashi ɗaya bisa goma na zakka zuwa gidan Allahnmu, su kawo a ɗakunan ajiya na baitulmali.
При левитах, когда они будут брать левитскую десятину, будет находиться священник, сын Аарона, чтобы левиты десятину из своих десятин отвозили в дом Бога нашего в комнаты, отделенные для кладовой,
39 Mutanen Isra’ila haɗe da Lawiyawa, za su kawo sadakokinsu na hatsi, sabon ruwan inabi da mai a ɗakunan ajiya inda ake ajiyar kayayyakin wuri mai tsarki da kuma inda firistoci, matsaran ƙofofi da kuma mawaƙa suke zama. “Ba za mu ƙyale gidan Allahnmu ba.”
потому что в эти комнаты как сыны Израилевы, так и левиты должны доставлять приносимое в дар: хлеб, вино и масло. Там священные сосуды, и служащие священники, и привратники, и певцы. И мы не оставим дома Бога нашего.