< Nehemiya 10 >

1 Waɗanda suka buga hatimin su ne, Nehemiya ɗan Hakaliya, wanda yake gwamna. Zedekiya
Et à la tête de ceux qui la scellèrent furent Néhémias artasastha, fils d'Achalias, et Sédécias,
2 da Serahiya, da Azariya, da Irmiya,
Fils d'Araïas, et Azarias, et Jérémie,
3 da Fashhur, da Amariya, da Malkiya,
Phasur, Amarias, Melchias,
4 da Hattush, da Shebaniya, da Malluk,
Attus, Sebani, Maluch,
5 da Harim, da Meremot, da Obadiya,
Iram, Meramoth, Abdia,
6 da Daniyel, da Ginneton, da Baruk,
Daniel, Gannathon, Baruch,
7 da Meshullam, da Abiya, da Miyamin,
Mesulam, Abia, Miamin,
8 da Ma’aziya, da Bilgai, da kuma Shemahiya. Waɗannan su ne Firistocin.
Maazia, Belgaï, Samaïa, tous ceux-là prêtres.
9 Lawiyawan kuwa su ne, Yeshuwa ɗan Azaniya, da Binnuyi ɗan Henadad, da Kadmiyel,
Puis les lévites: Josué, fils d'Azanias, Banaïu, des fils d'Enadad, Cadmiel;
10 ’yan’uwansu kuwa su ne, Shebaniya, da Hodiya, da Kelita, da Felahiya, da Hanan,
Et ses frères Sabanias, Oduïa, Calitan, Phélia, Anan,
11 da Mika, da Rehob, da Hashabiya,
Micha, Roob, Asébias,
12 da Zakkur, da Sherebiya, da Shebaniya,
Zacchor, Sarabia, Sebania,
13 da Hodiya, da Bani da kuma Beninu.
Odum; les fils de Banuaï,
14 Shugabannin mutane su ne, Farosh, da Fahat-Mowab, da Elam, da Zattu, da Bani,
Chefs du peuple: Pharos, Phaath-Moab, Zathuïa, fils de Bani,
15 da Bunni, da Azgad, da Bebai,
Asgad, Bébaï,
16 da Adoniya, da Bigwai, da Adin,
Adania, Bagoï, Hédin,
17 da Ater, da Hezekiya, da Azzur,
Ater, Ezéchias, Azur,
18 da Hodiya, da Hashum, da Bezai,
Oduïa, Esam, Bési,
19 da Harif, da Anatot, da Nebai,
Ariph, Anathoth, Nobaï,
20 da Magfiyash, da Meshullam, da Hezir,
Megaphès, Mesollam, Hézir,
21 da Meshezabel, da Zadok, da Yadduwa
Mesozébel, Saduc, Jeddua,
22 da Felatiya, da Hanan, da Anahiya,
Phattia, Anan, Anaïa,
23 da Hosheya, da Hananiya, da Hasshub,
Osée, Ananias, Asub,
24 da Hallohesh, da Filha, da Shobek,
Aloès, Phalaï, Sobec,
25 da Rehum, da Hashabna, da Ma’asehiya
Reüm, Essabana, Maasia,
26 da Ahiya, da Hanan, da Anan,
Et Aïa, Ainan, Enam,
27 da Malluk, da Harim da kuma Ba’ana.
Maluch, Héram, Baana.
28 “Sauran mutane, wato, firistoci, Lawiyawa, matsaran ƙofofi, mawaƙa, ma’aikatan haikali da dukan waɗanda suka ware kansu daga maƙwabta saboda Dokar Allah, tare da matansu da dukan’ya’yansu maza da mata waɗanda za su iya fahimta,
Et tout le reste du peuple, les prêtres, les lévites, les portiers, les chantres, les Nathinéens et tous ceux qui s'étaient retirés des gentils de la terre, pour revenir à la loi de Dieu, et leurs femmes et leurs filles; tous ceux qui avaient savoir et intelligence,
29 dukan waɗannan yanzu suka sadu da manyan gari’yan’uwansu, suka rantse, cewa la’ana ta same su idan ba su kiyaye Dokar Allah da aka bayar ta wurin Musa bawan Allah su kuma mai da hankali ga yin biyayya da dukan umarnai, ƙa’idodi da farillan Ubangiji shugabanmu ba.
Furent pressants avec leurs frères, et les excitèrent par leurs malédictions; et ceux-ci s'engagèrent, par malédictions et serments, à marcher selon la loi que Dieu a donnée par la main de Moïse, serviteur de Dieu, à garder les jugements, les préceptes et les commandements du Seigneur;
30 “Mun yi alkawari ba za mu ba da’ya’yanmu mata aure ga mutanen da suke kewaye da mu ba, ba kuwa za mu auri’ya’yansu mata wa’ya’yanmu maza ba.
À ne point donner nos filles en mariage aux peuples de la terre, et à ne point prendre leurs filles pour nos fils.
31 “Sa’ad da maƙwabta suka kawo kayayyaki ko hatsi don su sayar a ranar Asabbaci, ba za mu saya daga gare su a ranar Asabbaci ko a rana mai tsarki ba. Kowace shekarar Asabbaci ba za mu nome ƙasa ba kuma za mu yafe kowane irin bashi.
Nous n'achèterons rien, avons-nous dit, aux peuples de la terre qui viendront vendre le jour du sabbat; nous ne trafiquerons, ni le jour du sabbat; ni les jours sanctifiés; nous remettrons les dettes la septième année.
32 “Mun ɗauka hakkin bin umarnai na ba da kashi ɗaya bisa uku na shekel kowace shekara don hidimar gidan Allahnmu.
Nous établirons une ordonnance afin de lever sur nous un tiers de drachme, par an, pour le service du temple de notre Dieu;
33 Za mu tanada burodin da ake ajiye a kan tebur; za mu ba da hadayun hatsi da hadayun ƙonawa na kullum; za mu ba da hadayun Asabbatai, da na bukukkuwan Sabon Wata da na bukukkuwan da aka ƙayyade; za mu ba da hadayu masu tsarki; za mu ba da hadayun zunubi don a yi kafara domin Isra’ila; mu kuma ba da abubuwan da ake bukata dukan domin ayyukan gidan Allahnmu.
Pour les pains de proposition, pour le sacrifice perpétuel, et pour l'holocauste perpétuel, tant des sabbats que des nouvelles lunes, pour les fêtes et les jours saints, pour les péchés, pour les hosties pacifiques et pour les travaux du temple de notre Dieu.
34 “Mu, firistoci, da Lawiyawa da kuma mutane, mun jefa ƙuri’a don a san lokacin da kowane iyalinmu zai kawo sadakar itace don ƙonewa a gidan Allahnmu a ƙayyadaddun lokuta a bagaden Ubangiji Allahnmu, kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka.
Nous avons ensuite jeté les sorts, entre les prêtres, les lévites et le peuple, par familles paternelles, pour régler l'oblation du bois dans le temple de notre Dieu, aux époques prescrites chaque année, pour faire les holocaustes sur l'autel du Seigneur notre Dieu, comme il est écrit en la loi;
35 “Mun kuma ɗauka hakkin kawo nunan fari na hatsinmu da kuma na kowane itace mai ba da’ya’ya a gidan Ubangiji kowace shekara.
Pour que nous apportions les prémices des champs, et des arbres à fruit d'année en année, dans le temple du Seigneur,
36 “Kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka, za mu kawo ɗan fari na’ya’yanmu maza da na garken shanunmu, da na tumakinmu, da kuma na awakinmu a gidan Allahnmu, don firistocin da suke aikin a can.
Et l'évaluation des fils premiers-nés, celle des premiers-nés des bêtes de somme, entre les mains des prêtres et des lévites de service dans le temple de Dieu; comme il est écrit en la loi, et les premiers-nés de nos bœufs et de nos brebis;
37 “Ban da haka ma, za mu kawo wa ɗakunan ajiyar gidan Allahnmu, abincinmu na farko daga ƙasa, na hadayun hatsinmu, na’ya’yan dukan itatuwanmu da kuma na sabon ruwan inabinmu da mai namu wa firistoci. Za mu kuma kawo zakkar hatsinmu wa Lawiyawa, gama Lawiyawa ne ke karɓan Zakka cikin dukan garuruwan da muke noma.
Et pour que nous apportions aux prêtres, pour le trésor du temple de Dieu, les prémices de notre blé, des fruits de nos arbres, du vin et de l'huile; et aux lévites la dîme de notre terre, et pour que les lévites perçoivent la dîme en toutes les villes de la terre que nous cultivons.
38 Firist wanda yake daga zuriyar Haruna zai raka Lawiyawa sa’ad da suke karɓan zakka, Lawiyawan kuma za su kawo kashi ɗaya bisa goma na zakka zuwa gidan Allahnmu, su kawo a ɗakunan ajiya na baitulmali.
Et nous avons dit: Le prêtre, fils d'Aaron, aura part avec le lévite à la dîme des lévites; et les lévites offriront le dixième de leur dîme dans le temple de notre Dieu, et dans le trésor du temple.
39 Mutanen Isra’ila haɗe da Lawiyawa, za su kawo sadakokinsu na hatsi, sabon ruwan inabi da mai a ɗakunan ajiya inda ake ajiyar kayayyakin wuri mai tsarki da kuma inda firistoci, matsaran ƙofofi da kuma mawaƙa suke zama. “Ba za mu ƙyale gidan Allahnmu ba.”
Car, les fils d'Israël et les fils de Lévi apporteront au trésor les prémices de leur blé, de leur vin, de leur huile; et c'est là que seront les vases saints, sous la garde des prêtres, des serviteurs du temple, des chantres et des portiers; et nous n'abandonnerons pas le temple de notre Dieu.

< Nehemiya 10 >