< Nehemiya 10 >
1 Waɗanda suka buga hatimin su ne, Nehemiya ɗan Hakaliya, wanda yake gwamna. Zedekiya
Parmi les signataires figuraient: Néhémie, le gouverneur, fils de Hakhalia, et Sédécias;
2 da Serahiya, da Azariya, da Irmiya,
Seraia, Azaria, Jérémie;
3 da Fashhur, da Amariya, da Malkiya,
Pachhour, Amarla, Malkla;
4 da Hattush, da Shebaniya, da Malluk,
Hattouch, Chebania, Mallouc;
5 da Harim, da Meremot, da Obadiya,
Harim, Merémot, Obadia;
6 da Daniyel, da Ginneton, da Baruk,
Daniel, Ghinnetôn, Baruch;
7 da Meshullam, da Abiya, da Miyamin,
Mechoullam, Abia, Miyamin;
8 da Ma’aziya, da Bilgai, da kuma Shemahiya. Waɗannan su ne Firistocin.
Maazia, Bilgaï, Chemaïa; voilà pour les prêtres.
9 Lawiyawan kuwa su ne, Yeshuwa ɗan Azaniya, da Binnuyi ɗan Henadad, da Kadmiyel,
Pour les Lévites: Yêchoua, fils d’Azania, Binnoui, des fils de Hênadad, Kadmiêl;
10 ’yan’uwansu kuwa su ne, Shebaniya, da Hodiya, da Kelita, da Felahiya, da Hanan,
leurs frères; Chebania, Hodia, Kelita, Pelaia, Hanân;
11 da Mika, da Rehob, da Hashabiya,
Mikha, Rehob, Hachabia;
12 da Zakkur, da Sherebiya, da Shebaniya,
Zaccour, Chèrèbia, Chebania;
13 da Hodiya, da Bani da kuma Beninu.
Hodia, Bâni, Beninou.
14 Shugabannin mutane su ne, Farosh, da Fahat-Mowab, da Elam, da Zattu, da Bani,
Les chefs du peuple: Paroch, Pahat-Moab, Elam, Zattou, Bâni;
15 da Bunni, da Azgad, da Bebai,
Bounni, Azgad, Bêbai;
16 da Adoniya, da Bigwai, da Adin,
Adonia, Bigvaï, Adîn;
17 da Ater, da Hezekiya, da Azzur,
Atér, Hizkia, Azzour;
18 da Hodiya, da Hashum, da Bezai,
Hodia, Hachoum, Bêçaï;
19 da Harif, da Anatot, da Nebai,
Harif, Anatot, Nêbai;
20 da Magfiyash, da Meshullam, da Hezir,
Magpiach, Mechoullam, Hêzir;
21 da Meshezabel, da Zadok, da Yadduwa
Mechêzabel, Çadok, Yaddoua;
22 da Felatiya, da Hanan, da Anahiya,
Pelatia, Hanân, Anaïa;
23 da Hosheya, da Hananiya, da Hasshub,
Hochêa, Hanania, Hachoub;
24 da Hallohesh, da Filha, da Shobek,
Halohech, Pilha, Chobek;
25 da Rehum, da Hashabna, da Ma’asehiya
Rehoum, Hachabna, Maassèya;
26 da Ahiya, da Hanan, da Anan,
Ahiya, Hanân, Anân;
27 da Malluk, da Harim da kuma Ba’ana.
Mallouc, Harim et Baana.
28 “Sauran mutane, wato, firistoci, Lawiyawa, matsaran ƙofofi, mawaƙa, ma’aikatan haikali da dukan waɗanda suka ware kansu daga maƙwabta saboda Dokar Allah, tare da matansu da dukan’ya’yansu maza da mata waɗanda za su iya fahimta,
Et le reste du peuple, les prêtres, les Lévites, les portiers, les chanteurs, les serviteurs du temple, tous ceux qui s’étaient séparés des populations des pays pour se rallier à la loi de Dieu, leurs femmes, leurs fils, leurs filles et tous ceux qui étaient capables de comprendre,
29 dukan waɗannan yanzu suka sadu da manyan gari’yan’uwansu, suka rantse, cewa la’ana ta same su idan ba su kiyaye Dokar Allah da aka bayar ta wurin Musa bawan Allah su kuma mai da hankali ga yin biyayya da dukan umarnai, ƙa’idodi da farillan Ubangiji shugabanmu ba.
se joignirent à leurs frères, les personnages notables, et s’engagèrent par un serment solennel à suivre la loi de Dieu, qui avait été donnée par l’organe de Moïse, serviteur de Dieu, à observer et à pratiquer tous les commandements de l’Eternel, notre Seigneur, ses statuts et ses ordonnances;
30 “Mun yi alkawari ba za mu ba da’ya’yanmu mata aure ga mutanen da suke kewaye da mu ba, ba kuwa za mu auri’ya’yansu mata wa’ya’yanmu maza ba.
à ne pas marier nos filles avec les populations païennes du pays et à ne pas faire épouser leurs filles par nos fils;
31 “Sa’ad da maƙwabta suka kawo kayayyaki ko hatsi don su sayar a ranar Asabbaci, ba za mu saya daga gare su a ranar Asabbaci ko a rana mai tsarki ba. Kowace shekarar Asabbaci ba za mu nome ƙasa ba kuma za mu yafe kowane irin bashi.
et, au cas où les populations du pays viendraient débiter des marchandises et des denrées quelconques le jour du sabbat, à ne rien leur acheter ni ce jour ni les autres jours consacrés; à laisser, la septième année, chômer la terre et périmer toute créance.
32 “Mun ɗauka hakkin bin umarnai na ba da kashi ɗaya bisa uku na shekel kowace shekara don hidimar gidan Allahnmu.
De plus, nous nous soumîmes à l’obligation de nous imposer, chaque année, un tiers de sicle pour le service du temple de notre Dieu,
33 Za mu tanada burodin da ake ajiye a kan tebur; za mu ba da hadayun hatsi da hadayun ƙonawa na kullum; za mu ba da hadayun Asabbatai, da na bukukkuwan Sabon Wata da na bukukkuwan da aka ƙayyade; za mu ba da hadayu masu tsarki; za mu ba da hadayun zunubi don a yi kafara domin Isra’ila; mu kuma ba da abubuwan da ake bukata dukan domin ayyukan gidan Allahnmu.
pour le pain de proposition, l’oblation perpétuelle et l’holocauste perpétuel les sacrifices des sabbats, des néoménies et autres solennités, les offrandes sacrées, les expiatoires destinés à faire propitiation en faveur d’Israël; et tous les travaux de la maison de notre Dieu.
34 “Mu, firistoci, da Lawiyawa da kuma mutane, mun jefa ƙuri’a don a san lokacin da kowane iyalinmu zai kawo sadakar itace don ƙonewa a gidan Allahnmu a ƙayyadaddun lokuta a bagaden Ubangiji Allahnmu, kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka.
Nous désignâmes aussi, par la voie du sort, les prêtres, les Lévites et les gens du peuple chargés d’apporter l’offrande du bois au temple de notre Dieu, dans cette maison de nos ancêtres, année par année, à des époques déterminées, afin d’entretenir le feu sur l’autel de l’Eternel, notre Dieu, comme cela est prescrit dans la Thora.
35 “Mun kuma ɗauka hakkin kawo nunan fari na hatsinmu da kuma na kowane itace mai ba da’ya’ya a gidan Ubangiji kowace shekara.
Nous promîmes aussi d’apporter les prémices de notre sol et les prémices de tous les fruits des arbres, année par année, dans le temple de l’Eternel;
36 “Kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka, za mu kawo ɗan fari na’ya’yanmu maza da na garken shanunmu, da na tumakinmu, da kuma na awakinmu a gidan Allahnmu, don firistocin da suke aikin a can.
d’observer pour les premiers-nés de nos fils et de nos animaux ce qui est écrit dans la Thora; d’amener les premiers-nés de notre gros et de notre menu bétail au temple de notre Dieu, pour les prêtres qui font le service dans le temple de notre Dieu;
37 “Ban da haka ma, za mu kawo wa ɗakunan ajiyar gidan Allahnmu, abincinmu na farko daga ƙasa, na hadayun hatsinmu, na’ya’yan dukan itatuwanmu da kuma na sabon ruwan inabinmu da mai namu wa firistoci. Za mu kuma kawo zakkar hatsinmu wa Lawiyawa, gama Lawiyawa ne ke karɓan Zakka cikin dukan garuruwan da muke noma.
d’apporter pour les prêtres, dans les salles de la maison de notre Dieu, la première part de nos pâtes et nos prélèvements des fruits de tous les arbres, du moût et de l’huile, ainsi que la dîme de notre sol pour les Lévites. Et ce sont ces mêmes Lévites qui devront recueillir la dîme dans toutes nos villes agricoles.
38 Firist wanda yake daga zuriyar Haruna zai raka Lawiyawa sa’ad da suke karɓan zakka, Lawiyawan kuma za su kawo kashi ɗaya bisa goma na zakka zuwa gidan Allahnmu, su kawo a ɗakunan ajiya na baitulmali.
II fut convenu qu’un prêtre, descendant d’Aaron, assisterait les Lévites, quand ceux-ci prélèveraient la dîme, et que les Lévites transporteraient la dîme de la dîme dans le temple de notre Dieu, dans les salles de la maison du trésor.
39 Mutanen Isra’ila haɗe da Lawiyawa, za su kawo sadakokinsu na hatsi, sabon ruwan inabi da mai a ɗakunan ajiya inda ake ajiyar kayayyakin wuri mai tsarki da kuma inda firistoci, matsaran ƙofofi da kuma mawaƙa suke zama. “Ba za mu ƙyale gidan Allahnmu ba.”
Car c’est dans ces salles que les enfants d’Israël et les fils de Lévi devaient apporter le tribut du blé, du moût et de l’huile; là aussi devaient se trouver les ustensiles du sanctuaire et les prêtres de service, les portiers et les chanteurs. De la sorte, nous ne délaisserons pas la maison de notre Dieu.