< Nehemiya 10 >
1 Waɗanda suka buga hatimin su ne, Nehemiya ɗan Hakaliya, wanda yake gwamna. Zedekiya
And with those whose seal was affixed were, Nehemiah the Tirshatha the son of Chachalyah, and Zidkiyah.
2 da Serahiya, da Azariya, da Irmiya,
[Then] Serayah, 'Azaryah, Jeremiah,
3 da Fashhur, da Amariya, da Malkiya,
Pashchui, Amaryah, Malkiyah,
4 da Hattush, da Shebaniya, da Malluk,
Chattush, Shebanyah, Malluch,
5 da Harim, da Meremot, da Obadiya,
Charim, Meremoth, 'Obadiah,
6 da Daniyel, da Ginneton, da Baruk,
Daniel, Ginnethon, Baruch,
7 da Meshullam, da Abiya, da Miyamin,
Meshullam, Abiyah, Miyamin,
8 da Ma’aziya, da Bilgai, da kuma Shemahiya. Waɗannan su ne Firistocin.
Ma'azyah, Bilgai, Shema'yah: these were the priests.
9 Lawiyawan kuwa su ne, Yeshuwa ɗan Azaniya, da Binnuyi ɗan Henadad, da Kadmiyel,
And the Levites: Jeshua' the son of Azanyah, Binnui [[of]] the sons of Chenadad, Kadmiel;
10 ’yan’uwansu kuwa su ne, Shebaniya, da Hodiya, da Kelita, da Felahiya, da Hanan,
And their brethren, Shebanyah, Hodiyah, Kelita, Palayah, Chanan,
11 da Mika, da Rehob, da Hashabiya,
Micha, Rechob, Chashabyah,
12 da Zakkur, da Sherebiya, da Shebaniya,
Zaccur, Sherebyah, Shebanyah,
13 da Hodiya, da Bani da kuma Beninu.
Hodiyah, Bani, Beninu.
14 Shugabannin mutane su ne, Farosh, da Fahat-Mowab, da Elam, da Zattu, da Bani,
The chiefs of the people: Par'osh, Pachath-moab, 'Elam, Zatthu, Bani,
15 da Bunni, da Azgad, da Bebai,
Bunni, 'Azgad, Bebai,
16 da Adoniya, da Bigwai, da Adin,
Adoniyah, Bigvai, 'Adin,
17 da Ater, da Hezekiya, da Azzur,
Ater, Chizkiyah, 'Azzur,
18 da Hodiya, da Hashum, da Bezai,
Hodiyah, Chashum, Bezai,
19 da Harif, da Anatot, da Nebai,
Chariph, 'Anathoth, Nebai,
20 da Magfiyash, da Meshullam, da Hezir,
Magpi'ash, Meshullam, Chezir,
21 da Meshezabel, da Zadok, da Yadduwa
Meshezabel, Zadok, Jaddua',
22 da Felatiya, da Hanan, da Anahiya,
Pelatyah, Chanan, 'Anayah,
23 da Hosheya, da Hananiya, da Hasshub,
Hoshea', Chanayah, Chasshub,
24 da Hallohesh, da Filha, da Shobek,
Hallochesh, Pilcha, Shobek,
25 da Rehum, da Hashabna, da Ma’asehiya
Rechum, Chashabnah, Ma'asseyah,
26 da Ahiya, da Hanan, da Anan,
And Achiyah, Chanan, 'Anan,
27 da Malluk, da Harim da kuma Ba’ana.
Malluch, Charim, Ba'anah.
28 “Sauran mutane, wato, firistoci, Lawiyawa, matsaran ƙofofi, mawaƙa, ma’aikatan haikali da dukan waɗanda suka ware kansu daga maƙwabta saboda Dokar Allah, tare da matansu da dukan’ya’yansu maza da mata waɗanda za su iya fahimta,
And the rest of the people, the priests, the Levites, the gate-keepers, the singers, the temple-servants, and all those that had separated themselves from the nations of the lands unto the law of God, their wives, their sons, and their daughters, every one having knowledge, and having understanding,
29 dukan waɗannan yanzu suka sadu da manyan gari’yan’uwansu, suka rantse, cewa la’ana ta same su idan ba su kiyaye Dokar Allah da aka bayar ta wurin Musa bawan Allah su kuma mai da hankali ga yin biyayya da dukan umarnai, ƙa’idodi da farillan Ubangiji shugabanmu ba.
Held firmly with their brethren, their nobles, and entered into a curse, and into an oath, to walk in the law of God, which was given through means of Moses the servant of God, and to observe and to do all the commandments of the Eternal One, our Lord, and his ordinances and his statutes;
30 “Mun yi alkawari ba za mu ba da’ya’yanmu mata aure ga mutanen da suke kewaye da mu ba, ba kuwa za mu auri’ya’yansu mata wa’ya’yanmu maza ba.
And that we would not give our daughters unto the people of the land, nor take their daughters for our sons;
31 “Sa’ad da maƙwabta suka kawo kayayyaki ko hatsi don su sayar a ranar Asabbaci, ba za mu saya daga gare su a ranar Asabbaci ko a rana mai tsarki ba. Kowace shekarar Asabbaci ba za mu nome ƙasa ba kuma za mu yafe kowane irin bashi.
And that if the people of the land should bring wares or any provisions on the sabbath day to sell, we would not buy of them on the sabbath, or on [another] holy day; and that we would leave [the fields without reaping in] the seventh year, and [give up] every loan of hand.
32 “Mun ɗauka hakkin bin umarnai na ba da kashi ɗaya bisa uku na shekel kowace shekara don hidimar gidan Allahnmu.
And we established for us as one of the commandments to impose on ourselves [to give] the third part of a shekel in every year for the service of the house of our God;
33 Za mu tanada burodin da ake ajiye a kan tebur; za mu ba da hadayun hatsi da hadayun ƙonawa na kullum; za mu ba da hadayun Asabbatai, da na bukukkuwan Sabon Wata da na bukukkuwan da aka ƙayyade; za mu ba da hadayu masu tsarki; za mu ba da hadayun zunubi don a yi kafara domin Isra’ila; mu kuma ba da abubuwan da ake bukata dukan domin ayyukan gidan Allahnmu.
For the shew-bread, and for the continual meat-offering, and for the continual burnt-offering, [for those of] the sabbaths, of the new-moons, for the appointed feasts, and for the holy things, and for the sin-offerings to make an atonement for Israel, and [for] all the work of the house of our God.
34 “Mu, firistoci, da Lawiyawa da kuma mutane, mun jefa ƙuri’a don a san lokacin da kowane iyalinmu zai kawo sadakar itace don ƙonewa a gidan Allahnmu a ƙayyadaddun lokuta a bagaden Ubangiji Allahnmu, kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka.
And we, the priests, the Levites, and the people, cast lots concerning the procuring of the wood, to bring it into the house of our God, unto the house of our fathers, at fixed times, year by year, to burn upon the altar of the Lord our God, as it is written in the law;
35 “Mun kuma ɗauka hakkin kawo nunan fari na hatsinmu da kuma na kowane itace mai ba da’ya’ya a gidan Ubangiji kowace shekara.
And to bring the first-fruits of our ground, and the first-fruits of all fruit of all trees, year by year, unto the house of the Lord;
36 “Kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka, za mu kawo ɗan fari na’ya’yanmu maza da na garken shanunmu, da na tumakinmu, da kuma na awakinmu a gidan Allahnmu, don firistocin da suke aikin a can.
And also the first-born of our sons, and for our [unclean] cattle, as it is written in the law, and to bring the first-born of our herds and of our flocks to the house of our God, unto the priests that minister in the house of our God;
37 “Ban da haka ma, za mu kawo wa ɗakunan ajiyar gidan Allahnmu, abincinmu na farko daga ƙasa, na hadayun hatsinmu, na’ya’yan dukan itatuwanmu da kuma na sabon ruwan inabinmu da mai namu wa firistoci. Za mu kuma kawo zakkar hatsinmu wa Lawiyawa, gama Lawiyawa ne ke karɓan Zakka cikin dukan garuruwan da muke noma.
And that we would bring the first portion of our dough, and our heave-offerings, and this of the fruit of all manner of trees, of wine and of oil, to the priests, unto the chambers of the house of our God, and the tithes of our ground unto the Levites; and that these same Levites should be the receivers of the tithes in all the cities of our land-tillage;
38 Firist wanda yake daga zuriyar Haruna zai raka Lawiyawa sa’ad da suke karɓan zakka, Lawiyawan kuma za su kawo kashi ɗaya bisa goma na zakka zuwa gidan Allahnmu, su kawo a ɗakunan ajiya na baitulmali.
And that the priest the son of Aaron should be with the Levites, when the Levites receive the tithes; and that the Levites should bring up the tithe of the tithes unto the house of our God, to the chambers, into the treasure-house.
39 Mutanen Isra’ila haɗe da Lawiyawa, za su kawo sadakokinsu na hatsi, sabon ruwan inabi da mai a ɗakunan ajiya inda ake ajiyar kayayyakin wuri mai tsarki da kuma inda firistoci, matsaran ƙofofi da kuma mawaƙa suke zama. “Ba za mu ƙyale gidan Allahnmu ba.”
For into the chambers shall the children of Israel and the children of Levi bring the heave-offering of the corn, of the new wine, and the oil, and there shall be the vessels of the sanctuary, and the priests that minister, and the gatekeepers, and the singers: and that we will not forsake the house of our God.