< Nehemiya 10 >

1 Waɗanda suka buga hatimin su ne, Nehemiya ɗan Hakaliya, wanda yake gwamna. Zedekiya
Joma noketo lwetgi kaka joneno e magi: Nehemia ma jatelo maduongʼ, ma wuod Hakalia. Zedekia,
2 da Serahiya, da Azariya, da Irmiya,
Seraya, Azaria, Jeremia,
3 da Fashhur, da Amariya, da Malkiya,
Pashur, Amaria, Malkija,
4 da Hattush, da Shebaniya, da Malluk,
Hatush, Shebania, Maluk,
5 da Harim, da Meremot, da Obadiya,
Harim, Meremoth, Obadia,
6 da Daniyel, da Ginneton, da Baruk,
Daniel, Ginethon, Baruk,
7 da Meshullam, da Abiya, da Miyamin,
Meshulam, Abija, Mijamin,
8 da Ma’aziya, da Bilgai, da kuma Shemahiya. Waɗannan su ne Firistocin.
Mazia, Bilgai kod Shemaya. Magi ema ne jodolo.
9 Lawiyawan kuwa su ne, Yeshuwa ɗan Azaniya, da Binnuyi ɗan Henadad, da Kadmiyel,
Jo-Lawi ne gin: Jeshua wuod Azania, Binui ma nyakwar Henadad, Kadmiel,
10 ’yan’uwansu kuwa su ne, Shebaniya, da Hodiya, da Kelita, da Felahiya, da Hanan,
kod jogo ma jatich kaachiel kodgi kaka: Shebania, Hodia, Kelita, Pelaya, Hanan,
11 da Mika, da Rehob, da Hashabiya,
Mika, Rehob, Hashabia,
12 da Zakkur, da Sherebiya, da Shebaniya,
Zakur, Sherebia, Shebania,
13 da Hodiya, da Bani da kuma Beninu.
Hodia, Bani kod Beninu.
14 Shugabannin mutane su ne, Farosh, da Fahat-Mowab, da Elam, da Zattu, da Bani,
Jotend oganda ne gin: Parosh, Pahath-Moab, Elam, Zatu, Bani,
15 da Bunni, da Azgad, da Bebai,
Buni, Azgad, Bebai,
16 da Adoniya, da Bigwai, da Adin,
Adonija, Bigvai, Adin,
17 da Ater, da Hezekiya, da Azzur,
Ater, Hezekia, Azur,
18 da Hodiya, da Hashum, da Bezai,
Hodia, Hashum, Bezai,
19 da Harif, da Anatot, da Nebai,
Harif, Anathoth, Nebai,
20 da Magfiyash, da Meshullam, da Hezir,
Magpiash, Meshulam, Hezir,
21 da Meshezabel, da Zadok, da Yadduwa
Meshezabel, Zadok, Jadua,
22 da Felatiya, da Hanan, da Anahiya,
Pelatia, Hanan, Anaya,
23 da Hosheya, da Hananiya, da Hasshub,
Hoshea, Hanania, Hashub,
24 da Hallohesh, da Filha, da Shobek,
Halohesh, Pilha, Shobek,
25 da Rehum, da Hashabna, da Ma’asehiya
Rehum, Hashabna, Maseya,
26 da Ahiya, da Hanan, da Anan,
Ahiya, Hanan, Anan,
27 da Malluk, da Harim da kuma Ba’ana.
Maluk, Harim kod Baana.
28 “Sauran mutane, wato, firistoci, Lawiyawa, matsaran ƙofofi, mawaƙa, ma’aikatan haikali da dukan waɗanda suka ware kansu daga maƙwabta saboda Dokar Allah, tare da matansu da dukan’ya’yansu maza da mata waɗanda za su iya fahimta,
“Joma moko duto ma gin, jodolo, jo-Lawi, jorit dhorangeye, jower, jotij hekalu, to gi jogo duto mane owalore koa kuom jogo mokiewo kodgi nikech Chik mar Nyasaye, kaachiel gi mondegi kod yawuotgi kod nyigi duto manyalo winjo tiend chike,
29 dukan waɗannan yanzu suka sadu da manyan gari’yan’uwansu, suka rantse, cewa la’ana ta same su idan ba su kiyaye Dokar Allah da aka bayar ta wurin Musa bawan Allah su kuma mai da hankali ga yin biyayya da dukan umarnai, ƙa’idodi da farillan Ubangiji shugabanmu ba.
noriwore gi owetegi ma joka ruoth mi gikwongʼore giduto kendo negikwongʼore ni ginilu Chike Nyasaye, mane ochiwo kokalo kuom Musa jatichne kendo ginirit chike duto gi yore duto kod puonj mag Jehova Nyasaye Ruodhwa.
30 “Mun yi alkawari ba za mu ba da’ya’yanmu mata aure ga mutanen da suke kewaye da mu ba, ba kuwa za mu auri’ya’yansu mata wa’ya’yanmu maza ba.
“Wasingore ni ok wanachiw nyiwa mondo okendi gi jogo modak mokiewo kodwa to kata mana mondo yawuotwa okend nyigi.
31 “Sa’ad da maƙwabta suka kawo kayayyaki ko hatsi don su sayar a ranar Asabbaci, ba za mu saya daga gare su a ranar Asabbaci ko a rana mai tsarki ba. Kowace shekarar Asabbaci ba za mu nome ƙasa ba kuma za mu yafe kowane irin bashi.
“Ka jogo modak machiegni kodwa okelo gigegi mag ohala kata chambgi mondo giusi chiengʼ Sabato, ok wabi ngʼiewo kodgi chiengʼ Sabato kata e odiechiengʼ moro maler. E higa mar abiriyo ka mar abiriyo wabiro weyo tiyo e puodho kendo wabiro weyone ji gopegi duto.
32 “Mun ɗauka hakkin bin umarnai na ba da kashi ɗaya bisa uku na shekel kowace shekara don hidimar gidan Allahnmu.
“Higa ka higa wabiro kawo tingʼ mar kelo osuru madirom achiel kuom adek mar shekel ne tij od Nyasachwa,
33 Za mu tanada burodin da ake ajiye a kan tebur; za mu ba da hadayun hatsi da hadayun ƙonawa na kullum; za mu ba da hadayun Asabbatai, da na bukukkuwan Sabon Wata da na bukukkuwan da aka ƙayyade; za mu ba da hadayu masu tsarki; za mu ba da hadayun zunubi don a yi kafara domin Isra’ila; mu kuma ba da abubuwan da ake bukata dukan domin ayyukan gidan Allahnmu.
mibiro ngʼiewogo makati miketo e nyim Nyasaye pile, gi misango mar cham mitimo pile, gi misengini miwangʼo pep, kod misengini mamoko mitimo chiengʼ Sabato, kod mago mitimo ka dwe opor kod ndalo mag sewni moyier kendo ni tich misengini mamoko kod misengini mag golo richo jo-Israel kaachiel gi tije duto mag od Nyasachwa.
34 “Mu, firistoci, da Lawiyawa da kuma mutane, mun jefa ƙuri’a don a san lokacin da kowane iyalinmu zai kawo sadakar itace don ƙonewa a gidan Allahnmu a ƙayyadaddun lokuta a bagaden Ubangiji Allahnmu, kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka.
“Wan; jodolo, gi jo-Lawi kaachiel gi ji mamoko wasegoyo ombulu mondo wayier chiengʼ ma dala ka dala biro chiwoe yien miwangʼogo misengini ewi kendo mar misango mar Jehova Nyasaye ma Nyasachwa e kinde moketi higa ka higa, mana kaka ondiki e Chik.
35 “Mun kuma ɗauka hakkin kawo nunan fari na hatsinmu da kuma na kowane itace mai ba da’ya’ya a gidan Ubangiji kowace shekara.
“Bende wachiwore mar kelo nyak mokwongo mar chambwa kod olemo moro amora higa ka higa e od Jehova Nyasaye.
36 “Kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka, za mu kawo ɗan fari na’ya’yanmu maza da na garken shanunmu, da na tumakinmu, da kuma na awakinmu a gidan Allahnmu, don firistocin da suke aikin a can.
“Wabiro kelo yawuotwa makayo kod dhowa gi rombwa mokwong nywol ni jodolo matiyo e od Nyasachwa mana kaka ondik e Chik.
37 “Ban da haka ma, za mu kawo wa ɗakunan ajiyar gidan Allahnmu, abincinmu na farko daga ƙasa, na hadayun hatsinmu, na’ya’yan dukan itatuwanmu da kuma na sabon ruwan inabinmu da mai namu wa firistoci. Za mu kuma kawo zakkar hatsinmu wa Lawiyawa, gama Lawiyawa ne ke karɓan Zakka cikin dukan garuruwan da muke noma.
“Bende wabiro kelo e kar keno mar od Nyasaye gik machalo kaka; chiembwa mokwongo mar lowo, chiwo mar chambwa, olembe mar yiendwa duto kod divai manyien; chiembwa mokwongo mar lowo, chiwo mar chambwa, olembe mag yiendwa duto kod divai manyien gi mo ni jodolo. Kendo wabiro kelo achiel kuom apar mag chambwa ni jo-Lawi, nikech gin ema oyienigi choko achiel kuom apar e mier duto ma watiyoe.
38 Firist wanda yake daga zuriyar Haruna zai raka Lawiyawa sa’ad da suke karɓan zakka, Lawiyawan kuma za su kawo kashi ɗaya bisa goma na zakka zuwa gidan Allahnmu, su kawo a ɗakunan ajiya na baitulmali.
Jadolo moa e anywola Harun nyaka dhi gi jo-Lawi sa ma gikawo achiel kuom apar, to jo-Lawi nyaka kel achiel kuom apar mar achiel kuom aparno e kuonde keno mag od Nyasachwa.
39 Mutanen Isra’ila haɗe da Lawiyawa, za su kawo sadakokinsu na hatsi, sabon ruwan inabi da mai a ɗakunan ajiya inda ake ajiyar kayayyakin wuri mai tsarki da kuma inda firistoci, matsaran ƙofofi da kuma mawaƙa suke zama. “Ba za mu ƙyale gidan Allahnmu ba.”
Jo-Israel kaachiel gi jo-Lawi, nyaka kel chiwo margi mar cham, divai manyien kod mo nyaka e kar keno kama gigo mag kama ler mar lemo ikanoe kendo kama jodolo, jorit dhorangeye kod jower odakie. “Ok wanajwangʼ od Nyasachwa.”

< Nehemiya 10 >