< Nehemiya 10 >

1 Waɗanda suka buga hatimin su ne, Nehemiya ɗan Hakaliya, wanda yake gwamna. Zedekiya
Og paa den forseglede Skrift underskreve: Nehemia, Hattirsatha, Hakalias Søn, og Zedekia,
2 da Serahiya, da Azariya, da Irmiya,
Seraja, Asaria, Jeremia,
3 da Fashhur, da Amariya, da Malkiya,
Pashur, Amaria, Malkia,
4 da Hattush, da Shebaniya, da Malluk,
Hattus, Sebanja, Malluk,
5 da Harim, da Meremot, da Obadiya,
Harim, Meremoth, Obadja,
6 da Daniyel, da Ginneton, da Baruk,
Daniel, Ginthon, Baruk,
7 da Meshullam, da Abiya, da Miyamin,
Mesullam, Abia, Mijamin,
8 da Ma’aziya, da Bilgai, da kuma Shemahiya. Waɗannan su ne Firistocin.
Maasia, Bilgaj, Semaja; disse vare Præsterne.
9 Lawiyawan kuwa su ne, Yeshuwa ɗan Azaniya, da Binnuyi ɗan Henadad, da Kadmiyel,
Og Leviterne vare: Jesua, Asanias Søn, Binnuj af Henadads Børn, Kadmiel,
10 ’yan’uwansu kuwa su ne, Shebaniya, da Hodiya, da Kelita, da Felahiya, da Hanan,
og deres Brødre: Sebanja, Hodija, Klita, Plaja, Hanan,
11 da Mika, da Rehob, da Hashabiya,
Mika, Rekob, Hasabja,
12 da Zakkur, da Sherebiya, da Shebaniya,
Sakur, Serebja, Sebanja,
13 da Hodiya, da Bani da kuma Beninu.
Hodija, Bani, Beninu.
14 Shugabannin mutane su ne, Farosh, da Fahat-Mowab, da Elam, da Zattu, da Bani,
De Øverste af Folket vare: Pareos, Pahath-Moab, Elam, Sathu, Bani,
15 da Bunni, da Azgad, da Bebai,
Bunni, Asgad, Bebaj,
16 da Adoniya, da Bigwai, da Adin,
Adonia, Bigevaj, Adin,
17 da Ater, da Hezekiya, da Azzur,
Ater, Hiskia, Assur,
18 da Hodiya, da Hashum, da Bezai,
Hodija, Hasum, Bezaj,
19 da Harif, da Anatot, da Nebai,
Harif, Anathoth, Nebaj,
20 da Magfiyash, da Meshullam, da Hezir,
Magpias, Mesullam, Hesir,
21 da Meshezabel, da Zadok, da Yadduwa
Mesesabeel, Zadok, Jaddua,
22 da Felatiya, da Hanan, da Anahiya,
Platja, Hanan, Anaja,
23 da Hosheya, da Hananiya, da Hasshub,
Hosea, Hanania, Hasub,
24 da Hallohesh, da Filha, da Shobek,
Halohes, Pilha, Sobek,
25 da Rehum, da Hashabna, da Ma’asehiya
Rehum, Hasabna, Maeseja
26 da Ahiya, da Hanan, da Anan,
og Ahia, Hanan, Anan,
27 da Malluk, da Harim da kuma Ba’ana.
Malluk, Harim, Baena.
28 “Sauran mutane, wato, firistoci, Lawiyawa, matsaran ƙofofi, mawaƙa, ma’aikatan haikali da dukan waɗanda suka ware kansu daga maƙwabta saboda Dokar Allah, tare da matansu da dukan’ya’yansu maza da mata waɗanda za su iya fahimta,
Og det øvrige Folk, Præsterne, Leviterne, Portnerne, Sangerne, de livegne og hver, som havde skilt sig fra Folkene i Landene for at følge Guds Lov, deres Hustruer, deres Sønner og deres Døtre, hver som havde Forstand og Indsigt,
29 dukan waɗannan yanzu suka sadu da manyan gari’yan’uwansu, suka rantse, cewa la’ana ta same su idan ba su kiyaye Dokar Allah da aka bayar ta wurin Musa bawan Allah su kuma mai da hankali ga yin biyayya da dukan umarnai, ƙa’idodi da farillan Ubangiji shugabanmu ba.
de holdt sig fast til deres Brødre, til de ansete iblandt dem, og gik under Forbandelse og Ed ind paa, at de vilde vandre i Guds Lov, som er given ved Mose, den Guds Tjener, og at de vilde holde og gøre alle Herrens, vor Herres, Bud og hans Befalinger og hans Skikke;
30 “Mun yi alkawari ba za mu ba da’ya’yanmu mata aure ga mutanen da suke kewaye da mu ba, ba kuwa za mu auri’ya’yansu mata wa’ya’yanmu maza ba.
og at vi ikke skulde give Folkene i Landet vore Døtre, ej heller tage deres Døtre til vore Sønner;
31 “Sa’ad da maƙwabta suka kawo kayayyaki ko hatsi don su sayar a ranar Asabbaci, ba za mu saya daga gare su a ranar Asabbaci ko a rana mai tsarki ba. Kowace shekarar Asabbaci ba za mu nome ƙasa ba kuma za mu yafe kowane irin bashi.
og naar Folkene i Landet førte Vare og alle Haande Korn til at sælge paa Sabbatsdagen, at vi da ikke vilde tage det af dem paa Sabbaten og paa Helligdage, og at vi vilde lade Marken hvile i det syvende Aar og give Henstand med alle Krav.
32 “Mun ɗauka hakkin bin umarnai na ba da kashi ɗaya bisa uku na shekel kowace shekara don hidimar gidan Allahnmu.
Og vi fastsatte det Bud for os, at give aarlig en tredje Del af en Sekel til vor Guds Hus's Tjeneste,
33 Za mu tanada burodin da ake ajiye a kan tebur; za mu ba da hadayun hatsi da hadayun ƙonawa na kullum; za mu ba da hadayun Asabbatai, da na bukukkuwan Sabon Wata da na bukukkuwan da aka ƙayyade; za mu ba da hadayu masu tsarki; za mu ba da hadayun zunubi don a yi kafara domin Isra’ila; mu kuma ba da abubuwan da ake bukata dukan domin ayyukan gidan Allahnmu.
til Skuebrød og det bestandige Madoffer og til det bestandige Brændoffer, dem paa Sabbaterne, Nymaanederne, til Højtidsofre og til de hellige Gaver og til Syndofrene til at gøre Forligelse for Israel og til al vor Guds Hus's Gerning.
34 “Mu, firistoci, da Lawiyawa da kuma mutane, mun jefa ƙuri’a don a san lokacin da kowane iyalinmu zai kawo sadakar itace don ƙonewa a gidan Allahnmu a ƙayyadaddun lokuta a bagaden Ubangiji Allahnmu, kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka.
Og vi kastede Lod om Gaven af Ved, Præsterne, Leviterne og Folket, at de skulde bringe det til vor Guds Hus, efter vore Fædrenehuse, paa bestemte Tider, aarligaars, til at brænde paa Herren vor Guds Alter, som det er skrevet i Loven.
35 “Mun kuma ɗauka hakkin kawo nunan fari na hatsinmu da kuma na kowane itace mai ba da’ya’ya a gidan Ubangiji kowace shekara.
Og vi fastsatte at fremføre vor Marks Førstegrøde og den første Grøde af al Frugt af alle Haande Træer, aarligaars, til Herrens Hus,
36 “Kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka, za mu kawo ɗan fari na’ya’yanmu maza da na garken shanunmu, da na tumakinmu, da kuma na awakinmu a gidan Allahnmu, don firistocin da suke aikin a can.
og de førstefødte af vore Sønner og af vore Dyr, som skrevet er i Loven; og de førstefødte af vort store Kvæg og smaa Kvæg skulde vi bringe til vor Guds Hus til Præsterne, som tjene i vor Guds Hus;
37 “Ban da haka ma, za mu kawo wa ɗakunan ajiyar gidan Allahnmu, abincinmu na farko daga ƙasa, na hadayun hatsinmu, na’ya’yan dukan itatuwanmu da kuma na sabon ruwan inabinmu da mai namu wa firistoci. Za mu kuma kawo zakkar hatsinmu wa Lawiyawa, gama Lawiyawa ne ke karɓan Zakka cikin dukan garuruwan da muke noma.
og det første af vor Dejg og vore Offergaver og alle Haande Træers Frugt, Most og Olie, skulde vi bringe til Præsterne, til Kamrene i vor Guds Hus, og Tienden af vor Mark til Leviterne, og Leviterne skulde selv tage Tiende i alle vore Stæder, hvor der var Agerbrug;
38 Firist wanda yake daga zuriyar Haruna zai raka Lawiyawa sa’ad da suke karɓan zakka, Lawiyawan kuma za su kawo kashi ɗaya bisa goma na zakka zuwa gidan Allahnmu, su kawo a ɗakunan ajiya na baitulmali.
og Præsten, Arons Søn, skulde være med Leviterne, naar Leviterne toge Tiende; og Leviterne skulde bringe Tiende af Tienden til vor Guds Hus, til Kamrene i Forraadshuset.
39 Mutanen Isra’ila haɗe da Lawiyawa, za su kawo sadakokinsu na hatsi, sabon ruwan inabi da mai a ɗakunan ajiya inda ake ajiyar kayayyakin wuri mai tsarki da kuma inda firistoci, matsaran ƙofofi da kuma mawaƙa suke zama. “Ba za mu ƙyale gidan Allahnmu ba.”
Thi Israels Børn og Levis Børn skulde bringe Gaven af Kornet, Mosten og Olien til Kamrene, fordi der ere Helligdommens Kar, og Præsterne, som tjene, og Portnerne og Sangerne, at vi ikke skulde forlade vor Guds Hus.

< Nehemiya 10 >