< Nahum 1 >
1 Jawabi game da Ninebe a littafin wahayin Nahum, mutumin Elkosh.
Une révélation sur Ninive. Le livre de la vision de Nahoum l'Elkoshite.
2 Ubangiji Allah mai kishi ne, mai sakayya kuma. Ubangiji Allah mai kishi ne, mai ɗaukar fansa kuma. Ubangiji yakan ɗauki fansa a kan maƙiyansa, yakan ci gaba da fushi a kan abokan gābansa.
Yahvé est un Dieu jaloux et vengeur. Yahvé se venge et il est plein de colère. Yahvé se venge de ses adversaires, et il entretient sa colère contre ses ennemis.
3 Ubangiji mai jinkirin fushi ne, mai iko duka kuma. Ubangiji ba zai bar masu zunubi babu horo ba. Hanyarsa tana cikin guguwa da kuma hadari, gizagizai kuwa su ne ƙurar ƙafafunsa.
Yahvé est lent à la colère et grand en puissance, et il ne laisse pas le coupable impuni. Yahvé agit dans le tourbillon et dans la tempête, et les nuages sont la poussière de ses pieds.
4 Yakan tsawata wa teku yă kuma busar da shi; yakan sa dukan koguna su kafe. Bashan da Karmel sun yi yaushi tohon Lebanon kuma ya koɗe.
Il repousse la mer et la met à sec, il assèche tous les fleuves. Le Basan et le Carmel dépérissent. La fleur du Liban dépérit.
5 Duwatsu suna rawan jiki a gabansa tuddai kuma sun narke. Duniya da dukan abin da yake cikinta suna rawan jiki a gabansa.
Devant lui, les montagnes tremblent, et les collines se fondent. La terre tremble en sa présence, Le monde et tous ceux qui l'habitent.
6 Wa zai iya tsaya wa fushinsa? Wa yake da ikon jimre wa zafin hasalarsa? Ana zuba fushinsa kamar wuta; aka kuma ragargaza duwatsu a gabansa.
Qui peut résister à sa colère? Qui peut supporter l'ardeur de sa colère? Sa colère se répand comme un feu, et les rochers se brisent sous ses coups.
7 Ubangiji nagari ne, mafaka kuma a lokacin wahala. Yana kula da waɗanda suka dogara gare shi,
Yahvé est bon, il est une forteresse au jour de la détresse, et il connaît ceux qui se réfugient en lui.
8 amma da ambaliyar ruwa zai kawo Ninebe ga ƙarshe; zai fafari maƙiyansa zuwa cikin duhu.
Mais, par une inondation débordante, il détruira sa demeure, et il poursuivra ses ennemis dans les ténèbres.
9 Dukan abin da suke ƙullawa game da Ubangiji zai kawo ga ƙarshe; wahala ba za tă sāke komowa ƙaro na biyu ba.
Que complotez-vous contre Yahvé? Il l'anéantira. L'affliction ne se lèvera pas une seconde fois.
10 Za su sarƙafe a ƙaya, za su kuma bugu da ruwan inabinsu; za a laƙume su kamar busasshiyar ciyawa.
Car, empêtrés comme des épines, ivres comme de leur boisson, ils sont consumés comme du chaume sec.
11 Daga cikinki, ya Ninebe wani ya fito wanda ya ƙulla wa Ubangiji makirci yana ba da mugayen shawarwari.
Il en est sorti de vous un qui médite le mal contre Yahvé, qui conseille la méchanceté.
12 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Ko da yake sun yi tarayya, suna kuma da yawa, za a yanke su, a kawar a su. Ko da yake na ba ki azaba, ya Yahuda, ba zan ƙara ba ki azaba ba.
Yahvé dit: « Même s'ils sont en pleine force et aussi nombreux, ils seront abattus et disparaîtront. Je t'ai humilié, mais je ne t'humilierai plus.
13 Yanzu zan karya karkiyarsu daga wuyanki in kuma tsittsinke sarƙar da suka ɗaura ki.”
Maintenant, je briserai son joug de dessus toi, et je romprai tes liens. »
14 Ubangiji ya ba da umarni game da ke Ninebe, “Ba za ki sami zuriyar da za tă ci gaba da sunanki ba. Zan rurrushe siffofin da kuka sassaƙa da kuma gumakan da kuka ƙera gumakan da suke a cikin haikalin allolinku. Zan shirya kabarinki, domin ke muguwa ce.”
Yahvé a donné un ordre à ton sujet: « Aucun descendant ne portera plus ton nom. De la maison de vos dieux, j'exterminerai l'image gravée et l'image en fusion. Je ferai votre tombeau, car vous êtes vils. »
15 Duba, can a bisa duwatsu, ga ƙafafu mai kawo labari mai daɗi, wanda yake shelar salama! Ki yi bukukkuwanki, ya Yahuda, ki kuma cika wa’adodinki. Mugaye ba za su ƙara mamaye ki ba; domin za a hallaka su ƙaƙaf.
Voici, sur les montagnes, les pieds de celui qui apporte de bonnes nouvelles, qui publie la paix! Garde tes fêtes, Juda! Accomplis tes vœux, car le méchant ne passera plus par toi. Il est exterminé.