< Nahum 1 >
1 Jawabi game da Ninebe a littafin wahayin Nahum, mutumin Elkosh.
The prophecy concerning Nineveh. The book of the prophecy of Nahum, the Elkoshite.
2 Ubangiji Allah mai kishi ne, mai sakayya kuma. Ubangiji Allah mai kishi ne, mai ɗaukar fansa kuma. Ubangiji yakan ɗauki fansa a kan maƙiyansa, yakan ci gaba da fushi a kan abokan gābansa.
Jehovah is a jealous God, and an avenger; Jehovah is an avenger, and full of wrath! Jehovah taketh vengeance on his adversaries, And keepeth indignation for his enemies!
3 Ubangiji mai jinkirin fushi ne, mai iko duka kuma. Ubangiji ba zai bar masu zunubi babu horo ba. Hanyarsa tana cikin guguwa da kuma hadari, gizagizai kuwa su ne ƙurar ƙafafunsa.
Jehovah is slow to anger, but great in power; He will by no means clear the guilty; Jehovah cometh in the whirlwind and the storm, And the clouds are the dust of his feet.
4 Yakan tsawata wa teku yă kuma busar da shi; yakan sa dukan koguna su kafe. Bashan da Karmel sun yi yaushi tohon Lebanon kuma ya koɗe.
He rebuketh the sea, and maketh it dry, And drieth up all the rivers. Bashan languisheth, and Carmel, And the flower of Lebanon languisheth.
5 Duwatsu suna rawan jiki a gabansa tuddai kuma sun narke. Duniya da dukan abin da yake cikinta suna rawan jiki a gabansa.
The mountains tremble before him, And the hills melt; The earth is moved at his presence, Yea, the world and all that dwell therein.
6 Wa zai iya tsaya wa fushinsa? Wa yake da ikon jimre wa zafin hasalarsa? Ana zuba fushinsa kamar wuta; aka kuma ragargaza duwatsu a gabansa.
Who can stand before his indignation, And who can abide before the fierceness of his anger? His fury is poured out like fire, And the rocks are cast down by him!
7 Ubangiji nagari ne, mafaka kuma a lokacin wahala. Yana kula da waɗanda suka dogara gare shi,
Jehovah is good, A stronghold in the day of trouble; He careth for them that trust in him;
8 amma da ambaliyar ruwa zai kawo Ninebe ga ƙarshe; zai fafari maƙiyansa zuwa cikin duhu.
But with an overwhelming flood will he make a full end of her place, And darkness shall pursue his enemies.
9 Dukan abin da suke ƙullawa game da Ubangiji zai kawo ga ƙarshe; wahala ba za tă sāke komowa ƙaro na biyu ba.
What do ye meditate against Jehovah? He will make a full end; Not the second time shall the calamity come.
10 Za su sarƙafe a ƙaya, za su kuma bugu da ruwan inabinsu; za a laƙume su kamar busasshiyar ciyawa.
For while they are entangled like thorns, And like those that are drunk with wine, They shall be devoured as stubble fully dry.
11 Daga cikinki, ya Ninebe wani ya fito wanda ya ƙulla wa Ubangiji makirci yana ba da mugayen shawarwari.
From thee hath gone forth one that devised evil against Jehovah; That meditated destruction.
12 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Ko da yake sun yi tarayya, suna kuma da yawa, za a yanke su, a kawar a su. Ko da yake na ba ki azaba, ya Yahuda, ba zan ƙara ba ki azaba ba.
Thus saith Jehovah: Though they be flourishing, and likewise many, Yet shall they be cut down, and pass away; I have afflicted thee, but I will afflict thee no more.
13 Yanzu zan karya karkiyarsu daga wuyanki in kuma tsittsinke sarƙar da suka ɗaura ki.”
For now will I break his yoke from off thee, And will burst thy bonds in sunder.
14 Ubangiji ya ba da umarni game da ke Ninebe, “Ba za ki sami zuriyar da za tă ci gaba da sunanki ba. Zan rurrushe siffofin da kuka sassaƙa da kuma gumakan da kuka ƙera gumakan da suke a cikin haikalin allolinku. Zan shirya kabarinki, domin ke muguwa ce.”
And concerning thee hath Jehovah given command, That thy name shall no more be sown. From the house of thy god I will cut off the graven image and the molten image; I will make thy grave; for thou hast become vile!
15 Duba, can a bisa duwatsu, ga ƙafafu mai kawo labari mai daɗi, wanda yake shelar salama! Ki yi bukukkuwanki, ya Yahuda, ki kuma cika wa’adodinki. Mugaye ba za su ƙara mamaye ki ba; domin za a hallaka su ƙaƙaf.
Behold upon the mountains the feet of him that bringeth good tidings, That publisheth peace! Keep, O Judah, thy feasts, perform thy vows! For no more shall the destroyer pass through thee; He is utterly consumed.