< Nahum 3 >

1 Kaiton birni mai zub da jini, wadda take cike da ƙarairayi, cike da ganima, wadda ba a rasa masu fāɗawa cikin wahala!
Terrible things will happen to [Nineveh], that city [that is full of people who] murder [MTY] and lie. [The city is] full of things that were seized [from other countries by their soldiers]; [their armies] continually [LIT] have acted brutally towards people whom they conquered.
2 Ku ji karar bulala da kwaramniyar ƙafafu, da sukuwar dawakai da girgizar kekunan yaƙi!
But [now listen to the enemy soldiers coming to attack Nineveh]; [listen to them] cracking their whips, and [listen to the] rattle of [their chariot] wheels! [Listen to] their galloping horses and their chariots as they bounce along!
3 Mahaya dawakai sun kunno kai, takuba suna walƙiya, māsu kuma suna ƙyali; ga ɗumbun da aka kashe ga tsibin matattu, gawawwaki ba iyaka, mutane suna tuntuɓe da gawawwaki,
[Look at their] flashing swords and glittering spears as the horsemen race forward! Many [people of Nineveh will be] killed; [there will be] piles of corpses, [with the result that] people will stumble over them.
4 duk saboda yawan sha’awace-sha’awacen karuwa, mai daɗin baki, uwargidan maita, wadda ta ɓad da al’ummai ta wurin karuwancinta ta kuma ɓad da mutane ta wurin maitancinta.
All [that will happen] because [Nineveh is like] [MET] a beautiful prostitute [who lures men to where they will be ruined]; [Nineveh is a beautiful city] which has attracted/enticed [people of] other nations [to come there]. [The people of Nineveh] taught those people [of other nations rituals of] magic, and caused them to become their slaves.
5 “Ina gāba da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kware fatarinki a idonki. Zan nuna wa al’ummai tsiraicinki, masarautai kuma kunyarki.
[So] the Commander of the armies of angels says to [the people of Nineveh]: “I am your enemy, and I will [cause the people in other] nations to see you [completely] humiliated like [MET] [women who have committed adultery are humiliated by] having their skirts lifted high, [with the result that] people can see their naked [bodies].
6 Zan watsa miki ƙazanta, in yi miki wulaƙanci in kuma mai da ke abin reni.
I will cause rubbish/garbage to be thrown at you; I will show [others] that I despise you very much, and I will cause you to be publicly ridiculed.
7 Duk wanda ya gan ki zai gudu daga gare ki yana cewa, ‘Ninebe ta lalace, wa zai yi makoki domin ta?’ Ina zan sami wani wanda zai yi miki ta’aziyya?”
All those who see you will turn their backs to you and say, ‘Nineveh is ruined, but absolutely no one [RHQ] will mourn for it.’ No one will regret Nineveh being destroyed!”
8 Kin fi Tebes ne da take a bakin Nilu, da ruwa yake kewaye da ita? Rafi shi ne kāriyarta, ruwanta kuma katanga.
Your city is certainly [RHQ] no safer than Thebes [city] was. [Thebes was an important city] beside the Nile [River]; the river was [like] [SIM] a wall that protected the city [DOU].
9 Kush da kuma Masar su ne ƙarfinta marar iyaka; Fut da Libiya suna cikin mataimakanta.
[The rulers of] Ethiopia and Egypt helped Thebes; there was no limit to their power. [The governments of the nearby countries of] Put and Libya were also allies of Thebes.
10 Duk da haka an tafi da ita ta kuma tafi bauta. Aka fyaɗa ƙanananta da ƙasa aka yayyanka su gunduwa-gunduwa a kan kowane titi. Aka jefa ƙuri’a a kan manyan mutanenta, aka daure manyan mutanenta da sarƙoƙi.
But Thebes was captured, and [its people were] (exiled/forced to go to other countries). Their babies were dashed to pieces in the streets [of the city]. [Enemy soldiers] (cast lots/threw small marked stones) to decide who would get each official in Thebes [to become his slave]. All the leaders of Thebes were fastened/tied by chains.
11 Ke ma za ki bugu, za ki ɓuya. Ki kuma nemi mafaka daga wurin abokin gāba.
You [people of Nineveh] will similarly become dazed and drunk, and you will search for places to hide [to escape] from your enemies.
12 Dukan kagarunki suna kama da itatuwan ɓaure da’ya’yansu da suka nuna. Da an girgiza, sai ɓaure su zuba a bakin mai sha.
[Your enemies will cause] the walls around your city to fall down like [SIM] the first figs that fall from fig trees [each year]. [Your city will be captured easily, like] [MET] [figs that fall] into the mouths [HYP] of those who shake the fig trees.
13 Dubi mayaƙanki, duk mata ne! Ƙofofin ƙasarki a buɗe suke ga abokan gābanki, wuta ta cinye madogaransu.
Look at your soldiers! They will be [as weak/helpless as] [MET] women! The gates of your city will be opened wide [to allow] your enemies [to enter them], [and then] the bars of those gates will be burned.
14 Ki ja ruwa gama za a kewaye ki da yaƙi. Ki ƙara ƙarfin kagaranki! Ki kwaɓa laka, ki sassaƙa turmi ki gyara abin yin tubali!
Store up water [now to use when] your enemies surround the city! Repair the forts! Dig up clay and trample it [to make it soft], and put it into molds to make bricks [to repair the walls]!
15 A can wuta za tă cinye ki; takobi zai sare ki, kuma kamar fāra, za a cinye ki. Ki riɓaɓɓanya kamar fāra, ki riɓaɓɓanya kamar fārin ɗango!
[Nevertheless, your enemies] will burn your [city]; they will kill you with their swords; they will kill you like [SIM] locusts [destroy crops].
16 Kin ƙara yawan masu kasuwancinki har sai da suka fi taurarin sama. Amma kamar fāra sun cinye ƙasar sa’an nan suka tashi, suka tafi.
In your [city] there are now very many merchants; [it seems that] there are more of them than there are stars. But [when your city is being destroyed, those merchants will take the valuable things and disappear] [like] [SIM] locusts that strip the leaves from plants and [then] fly away.
17 Masu tsaronki suna kama da fāri ɗango, shugabanninki sun yi cincirindo kamar fārin ɗango da suka sauka a kan bango a rana mai sanyi, amma da rana ta fito, duk za su tashi su tafi, ba kuma wanda ya san inda suka nufa.
Your leaders are [also] like a swarm of [SIM] locusts [DOU] that crowd together on the stone fences/walls on a cold day, and [then] fly away when the sun comes up, and no one knows where they have gone.
18 Ya sarkin Assuriya, makiyayanka sun yi barci; manyan mutanenka sun kwanta su huta. An watsar da mutanenka a cikin duwatsu, ba wanda zai tattaro su.
O King of Assyria, your officials will [all] be dead [EUP]; your important people will lie down and rest [forever]. Your people will be scattered over the mountains, and there will no one to gather them [together].
19 Ba abin da zai warkar da rauninka; rauninka ya yi muni. Duk wanda ya ji labarinka zai tafa hannuwansa saboda farin cikin fāɗuwarka, gama wane ne bai ji jiki a hannunka ba?
You [are like someone who] has a wound that cannot be healed; [it will be] a wound that causes him to die. And all those who hear about what has happened to you will clap their hands [joyfully]. [They will say, ] “Everyone has [RHQ] suffered because he continually was [very] cruel to us.”

< Nahum 3 >