< Nahum 3 >

1 Kaiton birni mai zub da jini, wadda take cike da ƙarairayi, cike da ganima, wadda ba a rasa masu fāɗawa cikin wahala!
Woe to the city of blood! She is all full of deceit and robbery; She ceaseth not from plunder.
2 Ku ji karar bulala da kwaramniyar ƙafafu, da sukuwar dawakai da girgizar kekunan yaƙi!
[[Hark!]] The noise of the whip! The noise of the rattling of the wheels, And of the prancing horses, And of the bounding chariots!
3 Mahaya dawakai sun kunno kai, takuba suna walƙiya, māsu kuma suna ƙyali; ga ɗumbun da aka kashe ga tsibin matattu, gawawwaki ba iyaka, mutane suna tuntuɓe da gawawwaki,
The horseman lifteth up the flame of the sword, And the lightning of the spear; There is a multitude of the slain; heaps of dead bodies; There is no end to the carcasses; they stumble over the carcasses.
4 duk saboda yawan sha’awace-sha’awacen karuwa, mai daɗin baki, uwargidan maita, wadda ta ɓad da al’ummai ta wurin karuwancinta ta kuma ɓad da mutane ta wurin maitancinta.
It is because of the many whoredoms of the harlot, The graceful beauty, the mistress of enchantments, That sold nations by her whoredoms, And kingdoms by her enchantments.
5 “Ina gāba da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kware fatarinki a idonki. Zan nuna wa al’ummai tsiraicinki, masarautai kuma kunyarki.
Behold, I am against thee, saith Jehovah of host, And I will lift up thy trail over thy face, And I will show the nations thy nakedness, And the kingdoms thy shame.
6 Zan watsa miki ƙazanta, in yi miki wulaƙanci in kuma mai da ke abin reni.
And I will cast abominable filth upon thee, And I will dishonor thee, and make thee a gazing-stock,
7 Duk wanda ya gan ki zai gudu daga gare ki yana cewa, ‘Ninebe ta lalace, wa zai yi makoki domin ta?’ Ina zan sami wani wanda zai yi miki ta’aziyya?”
And all that see thee shall flee from thee, And shall say, “Nineveh is laid waste; Who will bemoan her? Whence shall I seek comforters for thee?”
8 Kin fi Tebes ne da take a bakin Nilu, da ruwa yake kewaye da ita? Rafi shi ne kāriyarta, ruwanta kuma katanga.
Art thou better than No-Ammon, That dwelt by the rivers, That had the waters round about her, Whose fortress was the sea, And whose wall was from the waters?
9 Kush da kuma Masar su ne ƙarfinta marar iyaka; Fut da Libiya suna cikin mataimakanta.
Ethiopia and Egypt were her strength, a countless multitude; Phut and Lybia were thy helpers!
10 Duk da haka an tafi da ita ta kuma tafi bauta. Aka fyaɗa ƙanananta da ƙasa aka yayyanka su gunduwa-gunduwa a kan kowane titi. Aka jefa ƙuri’a a kan manyan mutanenta, aka daure manyan mutanenta da sarƙoƙi.
Yet was she carried away; she went into captivity; Her children were dashed in pieces at the head of all the streets; For her honorable men they cast lots, And all her great men were bound in chains.
11 Ke ma za ki bugu, za ki ɓuya. Ki kuma nemi mafaka daga wurin abokin gāba.
Thou also shalt drink to the full; Thou, too, shalt be hidden; Thou shalt seek a refuge from the enemy!
12 Dukan kagarunki suna kama da itatuwan ɓaure da’ya’yansu da suka nuna. Da an girgiza, sai ɓaure su zuba a bakin mai sha.
All thy strong-holds shall be like fig-trees with the first ripe figs; If they be shaken, they fall into the mouth of the eater.
13 Dubi mayaƙanki, duk mata ne! Ƙofofin ƙasarki a buɗe suke ga abokan gābanki, wuta ta cinye madogaransu.
Behold, thy people shall be women in the midst of thee; The gates of thy land shall be set wide open to thine enemies; The fire shall devour thy bars.
14 Ki ja ruwa gama za a kewaye ki da yaƙi. Ki ƙara ƙarfin kagaranki! Ki kwaɓa laka, ki sassaƙa turmi ki gyara abin yin tubali!
Draw thee water for the siege, Fortify thy strongholds. Go into the clay, and tread the mortar; Repair the brick-kiln!
15 A can wuta za tă cinye ki; takobi zai sare ki, kuma kamar fāra, za a cinye ki. Ki riɓaɓɓanya kamar fāra, ki riɓaɓɓanya kamar fārin ɗango!
Then shall the fire devour thee; The sword shall cut thee off, It shall devour thee like the locust; Though thou art increased like the locusts, Though thou art increased like the thick locusts.
16 Kin ƙara yawan masu kasuwancinki har sai da suka fi taurarin sama. Amma kamar fāra sun cinye ƙasar sa’an nan suka tashi, suka tafi.
Thy merchants have been more numerous than the stars of heaven; The locusts spread themselves and fly away.
17 Masu tsaronki suna kama da fāri ɗango, shugabanninki sun yi cincirindo kamar fārin ɗango da suka sauka a kan bango a rana mai sanyi, amma da rana ta fito, duk za su tashi su tafi, ba kuma wanda ya san inda suka nufa.
Thy princes are like locusts, And thy captains like swarms of locusts, Which encamp in the hedges in the time of cold; But when the sun ariseth, they flee away, And the place is not known where they are.
18 Ya sarkin Assuriya, makiyayanka sun yi barci; manyan mutanenka sun kwanta su huta. An watsar da mutanenka a cikin duwatsu, ba wanda zai tattaro su.
Thy shepherds slumber, O king of Assyria! Thy nobles take their rest, Thy people are scattered on the mountains, and none gathereth them.
19 Ba abin da zai warkar da rauninka; rauninka ya yi muni. Duk wanda ya ji labarinka zai tafa hannuwansa saboda farin cikin fāɗuwarka, gama wane ne bai ji jiki a hannunka ba?
Thy bruise is incurable; Thy wound is mortal. All that hear of thee shall clap their hands over thee; For upon whom hath not thy wickedness passed continually?

< Nahum 3 >