< Nahum 3 >
1 Kaiton birni mai zub da jini, wadda take cike da ƙarairayi, cike da ganima, wadda ba a rasa masu fāɗawa cikin wahala!
Woe to the city of blood! it is all full of lies and robbery; never ceaseth the preying;
2 Ku ji karar bulala da kwaramniyar ƙafafu, da sukuwar dawakai da girgizar kekunan yaƙi!
The noise of a whip, and the noise of the rattling of wheels, and of prancing horses, and of the skipping chariots.
3 Mahaya dawakai sun kunno kai, takuba suna walƙiya, māsu kuma suna ƙyali; ga ɗumbun da aka kashe ga tsibin matattu, gawawwaki ba iyaka, mutane suna tuntuɓe da gawawwaki,
Horsemen mount, and there are the flaming sword and the glittering spear: and there is a multitude of slain, and heaps of carcasses; and without end are the corpses; they stumble on their corpses;
4 duk saboda yawan sha’awace-sha’awacen karuwa, mai daɗin baki, uwargidan maita, wadda ta ɓad da al’ummai ta wurin karuwancinta ta kuma ɓad da mutane ta wurin maitancinta.
Because of the multitude of the lewd deeds of the harlot, that is rich in gracefulness, the mistress of witchcrafts, that selleth nations through her lewd deeds, and families through her witchcrafts.
5 “Ina gāba da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kware fatarinki a idonki. Zan nuna wa al’ummai tsiraicinki, masarautai kuma kunyarki.
Behold, I will be against thee, saith the Lord of hosts; and I will lay thy skirts open over thy face, and I will let nations see thy nakedness, and kingdoms thy shame.
6 Zan watsa miki ƙazanta, in yi miki wulaƙanci in kuma mai da ke abin reni.
And I will cast abominable filth upon thee, and defile thee, and will render thee a dirt-heap.
7 Duk wanda ya gan ki zai gudu daga gare ki yana cewa, ‘Ninebe ta lalace, wa zai yi makoki domin ta?’ Ina zan sami wani wanda zai yi miki ta’aziyya?”
And it shall come to pass, that all they that see thee shall flee from thee, and say, Laid waste is Nineveh: who will condole with her? whence shall I seek comforters for thee?
8 Kin fi Tebes ne da take a bakin Nilu, da ruwa yake kewaye da ita? Rafi shi ne kāriyarta, ruwanta kuma katanga.
Art thou better than No-amon, that was situated on the rivers, that had water round about her, the rampart of which was the sea, and the walls of which rose out of the sea?
9 Kush da kuma Masar su ne ƙarfinta marar iyaka; Fut da Libiya suna cikin mataimakanta.
Ethiopia the numerous, and Egypt that was without end, Put and Lubim were thy helpers.
10 Duk da haka an tafi da ita ta kuma tafi bauta. Aka fyaɗa ƙanananta da ƙasa aka yayyanka su gunduwa-gunduwa a kan kowane titi. Aka jefa ƙuri’a a kan manyan mutanenta, aka daure manyan mutanenta da sarƙoƙi.
Yet also she was exiled, was carried away into captivity; also her young children were dashed in pieces at the corners of all streets: and for her honorable men they cast lots, and all her great ones were bound with chains.
11 Ke ma za ki bugu, za ki ɓuya. Ki kuma nemi mafaka daga wurin abokin gāba.
Thou also shalt be made drunken, thou shalt be hidden from view: thou also shalt seek refuge because of the enemy.
12 Dukan kagarunki suna kama da itatuwan ɓaure da’ya’yansu da suka nuna. Da an girgiza, sai ɓaure su zuba a bakin mai sha.
All thy strong-holds shall be like fig-trees with the first ripe figs, which, if they be shaken, will fall into the mouth of the eater.
13 Dubi mayaƙanki, duk mata ne! Ƙofofin ƙasarki a buɗe suke ga abokan gābanki, wuta ta cinye madogaransu.
Behold, thy people are become women in the midst of thee: unto thy enemies are the gates of thy land set wide open; the fire hath devoured thy bars.
14 Ki ja ruwa gama za a kewaye ki da yaƙi. Ki ƙara ƙarfin kagaranki! Ki kwaɓa laka, ki sassaƙa turmi ki gyara abin yin tubali!
Water for the siege draw for thyself, fortify thy strongholds: go into the clay, and tread the mortar, make strong the brick-kiln.
15 A can wuta za tă cinye ki; takobi zai sare ki, kuma kamar fāra, za a cinye ki. Ki riɓaɓɓanya kamar fāra, ki riɓaɓɓanya kamar fārin ɗango!
There shall the fire devour thee; the sword shall cut thee off, it shall devour thee up like the cankerworm: [though] thou make thyself many as the cankerworm; make thyself many as the locusts.
16 Kin ƙara yawan masu kasuwancinki har sai da suka fi taurarin sama. Amma kamar fāra sun cinye ƙasar sa’an nan suka tashi, suka tafi.
[Though] thou hadst multiplied thy merchants more than the stars of heaven: the cankerworm spreadeth itself out, and flieth away.
17 Masu tsaronki suna kama da fāri ɗango, shugabanninki sun yi cincirindo kamar fārin ɗango da suka sauka a kan bango a rana mai sanyi, amma da rana ta fito, duk za su tashi su tafi, ba kuma wanda ya san inda suka nufa.
Thy crowned ones are like the locusts, and thy leaders like the swarms of locusts, which camp in the hedges on a cold day, but when the sun ariseth they flee away, and their place is not known where they are.
18 Ya sarkin Assuriya, makiyayanka sun yi barci; manyan mutanenka sun kwanta su huta. An watsar da mutanenka a cikin duwatsu, ba wanda zai tattaro su.
Thy shepherds slumber, O king of Assyria; thy valiant men are at rest: scattered are thy people upon the mountains, and there is none that gathereth them.
19 Ba abin da zai warkar da rauninka; rauninka ya yi muni. Duk wanda ya ji labarinka zai tafa hannuwansa saboda farin cikin fāɗuwarka, gama wane ne bai ji jiki a hannunka ba?
There is no healing for thy breach; fatal is thy wound: all that hear the report of thee will clap their hands over thee; for over whom did not thy wickedness pass continually?