< Nahum 2 >

1 Mai hari yana matsowa a kanki, Ninebe. Ki tsare mafaka, ki yi gadin hanya ki sha ɗamara ki tattaro dukan ƙarfinki!
Il monte, celui qui ravagera devant toi, qui maintiendra le siège; considère la voie, affermis tes reins, augmente extrêmement ta force.
2 Ubangiji zai maido da darajar Yaƙub, kamar ta Isra’ila, ko da yake masu washewa sun washe su suka kuma lalatar da inabinsu.
Parce que le Seigneur a rétabli la gloire de Jacob et la gloire d’Israël; parce que les dévastateurs les ont dispersés et ont gâté leurs rejetons.
3 Garkuwoyin sojojinsa ja wur ne; jarumawansa suna sanye da kaya masu ruwan jan garura. Ƙarafan kekunan yaƙi suna walƙiya a ranar da aka shirya su; ana kaɗa māsu da bantsoro.
Le bouclier de ses braves est de feu, les hommes de l’armée sont vêtus d’écarlate; les courroies de son char sont de feu, au jour de sa préparation au combat, et ceux qui le conduisent se sont assoupis.
4 Kekunan yaƙi sun zabura a tituna, suna kai da kawowa a dandali. Suna walƙiya kamar tocila suna sheƙawa a guje kamar walƙiya.
Sur les routes ils sont allés sans ordre; les quadriges se sont heurtés au milieu des places publiques; leur aspect était comme des lampes, comme des éclairs sillonnant les nues.
5 Ninebe ta tattara rundunarta, duk da haka sun yi ta tuntuɓe a kan hanyarsu. Sun ruga zuwa katangan birnin, sun sanya garkuwar kāriya a inda ya kamata.
Il se souviendra de ses braves; ils tomberont dans leurs marches; ils monteront rapidement sur ses murs, et il leur sera préparé un abri.
6 An buɗe ƙofofin rafuffukan sai wurin ya rurrushe.
Les portes des fleuves ont été ouvertes, et le temple a été renversé par terre.
7 An umarta cewa birnin za tă tafi bauta, za a kuma yi gaba da su. Bayi’yan mata suna kuka kamar tattabaru suna buga ƙirjinsu.
Et le soldat a été emmené captif, et ses servantes étaient conduites, gémissant comme des colombes et murmurant dans leurs cœurs.
8 Ninebe tana kama da tafki, wanda ruwanta yana yoyo. Suna kuka suna cewa, “Ku tsaya! Ku tsaya,” amma ba wanda ya waiga.
Et Ninive, ses eaux étaient comme une piscine d’eaux; mais eux ont pris la fuite: arrêtez, arrêtez, et il n’est personne qui revienne.
9 A washe azurfa; a washe zinariya; dukiyarsu ba ta da iyaka, arzikinsu kuma ba ya ƙarewa.
Pillez l’argent, pillez l’or; et ses richesses en toute sorte de choses précieuses sont sans fin.
10 Ta zama wofi, an washe ta, an tuɓe ta! Zukata sun narke, gwiwoyi suna kaɗuwa, jikuna suna rawa, fuskoki duk sun kwantsare!
Ninive a été dévastée, déchirée, mise en pièces, et le cœur s’est fondu, et il y a eu faiblesse dans les genoux, défaillance dans tous les reins; et les faces d’eux tous étaient comme le noir d’une marmite.
11 Ina kogon zakokin nan yake yanzu, inda suka ciyar da’ya’yansu, inda zaki da zakanya sukan shiga, da’ya’yansu, ba mai damunsu
Où est Ninive, demeure des lions, et propre au pâturage des petits des lions, vers laquelle allait le lion, afin d’y entrer, ainsi que le petit du lion, et il n’y a personne qui l’épouvante.
12 Zaki ya kashe abin da ya ishe’ya’yansa ya kuma murɗe wuyan dabbobi ya cika wurin zamansa da abin da ya kama ya cika kogwanninsa da abin da ya kashe.
Le lion a ramassé suffisamment pour ses petits, et a égorgé pour ses lionnes; et il a rempli de proie ses tanières, et son repaire de rapine.
13 “Ina gāba da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ƙone kekunan yaƙinki, takobi kuma zai fafare’ya’yan zakokinki. Ba kuma zan bar miki namun jejin da za ki kashe a duniya ba. Ba kuwa za a ƙara jin muryar’yan saƙonki ba.”
Voici que moi je viens à toi, dit le Seigneur des armées, et je mettrai le feu à tes quadriges, et je les réduirai en fumée, et le glaive dévorera tes lionceaux; et j’exterminerai de la terre ta proie, et l’on n’entendra plus la voix de tes messagers.

< Nahum 2 >