< Nahum 2 >

1 Mai hari yana matsowa a kanki, Ninebe. Ki tsare mafaka, ki yi gadin hanya ki sha ɗamara ki tattaro dukan ƙarfinki!
Le destructeur vient contre toi, Ninive! Garde la forteresse, surveille le chemin, fortifie tes reins, et rassemble toutes tes forces.
2 Ubangiji zai maido da darajar Yaƙub, kamar ta Isra’ila, ko da yake masu washewa sun washe su suka kuma lalatar da inabinsu.
Car l'Éternel rétablit la gloire de Jacob comme la gloire d'Israël, parce que les pillards les ont pillés et qu'ils ont ravagé leurs vignes.
3 Garkuwoyin sojojinsa ja wur ne; jarumawansa suna sanye da kaya masu ruwan jan garura. Ƙarafan kekunan yaƙi suna walƙiya a ranar da aka shirya su; ana kaɗa māsu da bantsoro.
Le bouclier de ses hommes vaillants est rouge; les guerriers sont vêtus d'écarlate; l'acier des chars étincelle, au jour où il se prépare, et les lances sont agitées.
4 Kekunan yaƙi sun zabura a tituna, suna kai da kawowa a dandali. Suna walƙiya kamar tocila suna sheƙawa a guje kamar walƙiya.
Les chars roulent avec furie dans les rues; ils se précipitent dans les places; à les voir ils sont comme des flambeaux, ils courent comme des éclairs!
5 Ninebe ta tattara rundunarta, duk da haka sun yi ta tuntuɓe a kan hanyarsu. Sun ruga zuwa katangan birnin, sun sanya garkuwar kāriya a inda ya kamata.
Le roi de Ninive se souvient de ses hommes vaillants; mais ils chancellent dans leur marche. Ils se hâtent vers la muraille, la défense est préparée.
6 An buɗe ƙofofin rafuffukan sai wurin ya rurrushe.
Les portes des fleuves sont ouvertes, et le palais s'écroule!
7 An umarta cewa birnin za tă tafi bauta, za a kuma yi gaba da su. Bayi’yan mata suna kuka kamar tattabaru suna buga ƙirjinsu.
C'en est fait! Elle est mise à nu, elle est emmenée, et ses servantes gémissent comme des colombes; elles se frappent la poitrine.
8 Ninebe tana kama da tafki, wanda ruwanta yana yoyo. Suna kuka suna cewa, “Ku tsaya! Ku tsaya,” amma ba wanda ya waiga.
Ninive était, depuis qu'elle existe, comme un réservoir plein d'eau. Ils fuient! ... Arrêtez! Arrêtez!... Mais personne ne se retourne!
9 A washe azurfa; a washe zinariya; dukiyarsu ba ta da iyaka, arzikinsu kuma ba ya ƙarewa.
Pillez l'argent! Pillez l'or! Car il n'y a point de fin à ses richesses, c'est une abondance de toutes sortes d'objets précieux.
10 Ta zama wofi, an washe ta, an tuɓe ta! Zukata sun narke, gwiwoyi suna kaɗuwa, jikuna suna rawa, fuskoki duk sun kwantsare!
Pillage, et ravage, et dévastation! Le cœur se fond, les genoux tremblent; la douleur est dans tous les reins, et tous les visages pâlissent.
11 Ina kogon zakokin nan yake yanzu, inda suka ciyar da’ya’yansu, inda zaki da zakanya sukan shiga, da’ya’yansu, ba mai damunsu
Où est maintenant ce repaire de lions? Où est ce lieu de pâture des lionceaux, où se retiraient le lion, la lionne et les petits du lion, sans que personne y vînt les troubler?
12 Zaki ya kashe abin da ya ishe’ya’yansa ya kuma murɗe wuyan dabbobi ya cika wurin zamansa da abin da ya kama ya cika kogwanninsa da abin da ya kashe.
Le lion déchirait pour ses petits; il étranglait pour ses lionnes; il remplissait de proies ses antres, et ses repaires de dépouilles.
13 “Ina gāba da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ƙone kekunan yaƙinki, takobi kuma zai fafare’ya’yan zakokinki. Ba kuma zan bar miki namun jejin da za ki kashe a duniya ba. Ba kuwa za a ƙara jin muryar’yan saƙonki ba.”
Voici, j'en veux à toi, dit l'Éternel des armées, je mettrai le feu à tes chars, et je les réduirai en fumée; l'épée dévorera tes lionceaux; j'arracherai du pays ta proie, et l'on n'entendra plus la voix de tes messagers.

< Nahum 2 >