< Nahum 2 >
1 Mai hari yana matsowa a kanki, Ninebe. Ki tsare mafaka, ki yi gadin hanya ki sha ɗamara ki tattaro dukan ƙarfinki!
Le destructeur s’avance contre toi: veille sur la forteresse, observe la route, affermis tes reins, ramasse toutes tes forces!
2 Ubangiji zai maido da darajar Yaƙub, kamar ta Isra’ila, ko da yake masu washewa sun washe su suka kuma lalatar da inabinsu.
Car le Seigneur rétablit la grandeur de Jacob comme la grandeur d’Israël, puisque des pillards les avaient dépouillés, et avaient ruiné leurs sarments.
3 Garkuwoyin sojojinsa ja wur ne; jarumawansa suna sanye da kaya masu ruwan jan garura. Ƙarafan kekunan yaƙi suna walƙiya a ranar da aka shirya su; ana kaɗa māsu da bantsoro.
Les boucliers de ses héros sont teints de rouge, ses hommes de guerre sont vêtus de pourpre. Ses chars jettent des éclats de flamme au jour où il les met en ligne, et les lances sont mises en mouvement.
4 Kekunan yaƙi sun zabura a tituna, suna kai da kawowa a dandali. Suna walƙiya kamar tocila suna sheƙawa a guje kamar walƙiya.
Les chars tourbillonnent dans les rues, bondissent à travers les places; à les voir, on dirait des torches, ils se précipitent comme des éclairs.
5 Ninebe ta tattara rundunarta, duk da haka sun yi ta tuntuɓe a kan hanyarsu. Sun ruga zuwa katangan birnin, sun sanya garkuwar kāriya a inda ya kamata.
Il s’en rapporte à ses braves: ils trébuchent dans leur marche, se hâtent vers les remparts de la ville, et on prépare l’abri couvert.
6 An buɗe ƙofofin rafuffukan sai wurin ya rurrushe.
Les portes protégées par les cours d’eau sont enfoncées et le palais en est atterré.
7 An umarta cewa birnin za tă tafi bauta, za a kuma yi gaba da su. Bayi’yan mata suna kuka kamar tattabaru suna buga ƙirjinsu.
Houzab la reine est tirée de sa cachette et emmenée, tandis que ses servantes poussent des soupirs, telles des colombes qui gémissent, et se frappent la poitrine.
8 Ninebe tana kama da tafki, wanda ruwanta yana yoyo. Suna kuka suna cewa, “Ku tsaya! Ku tsaya,” amma ba wanda ya waiga.
Or, Ninive était de tout temps comme un réservoir plein d’eau; et maintenant ils fuient! "Arrêtez! Tenez bon!" Mais personne ne se retourne.
9 A washe azurfa; a washe zinariya; dukiyarsu ba ta da iyaka, arzikinsu kuma ba ya ƙarewa.
Pillez de l’or! Pillez de l’argent! Infinis sont les trésors: c’est toute une richesse de vases précieux!
10 Ta zama wofi, an washe ta, an tuɓe ta! Zukata sun narke, gwiwoyi suna kaɗuwa, jikuna suna rawa, fuskoki duk sun kwantsare!
Tout est pillé, dépouillé, ravagé! Les cœurs se sentent défaillir, les genoux vacillent, tous les reins sont saisis de tremblement, tous les visages se couvrent de pâleur.
11 Ina kogon zakokin nan yake yanzu, inda suka ciyar da’ya’yansu, inda zaki da zakanya sukan shiga, da’ya’yansu, ba mai damunsu
Qu’est-il advenu de ce repaire de lions, où se gorgeaient les lionceaux, où se rencontraient lion, lionne et lionceau, que personne n’osait troubler?
12 Zaki ya kashe abin da ya ishe’ya’yansa ya kuma murɗe wuyan dabbobi ya cika wurin zamansa da abin da ya kama ya cika kogwanninsa da abin da ya kashe.
Le lion déchirait la proie pour ses petits, il l’étranglait pour ses lionnes; il remplissait ses antres de victuailles et ses tanières de bêtes mises en pièces.
13 “Ina gāba da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ƙone kekunan yaƙinki, takobi kuma zai fafare’ya’yan zakokinki. Ba kuma zan bar miki namun jejin da za ki kashe a duniya ba. Ba kuwa za a ƙara jin muryar’yan saƙonki ba.”
Voici, je m’apprête contre toi, dit l’Eternel-Cebaot: je brûlerai tes chars dans un nuage de fumée; tes lionceaux, le glaive les dévorera. Je mettrai fin à tes rapines sur la terre, et l’on n’entendra plus la voix de tes hérauts.