< Nahum 2 >

1 Mai hari yana matsowa a kanki, Ninebe. Ki tsare mafaka, ki yi gadin hanya ki sha ɗamara ki tattaro dukan ƙarfinki!
It is all over with him, he has been removed, [one] who has been delivered from affliction has come up panting into thy presence, watch the way, strengthen [thy] loins, be very valiant in [thy] strength.
2 Ubangiji zai maido da darajar Yaƙub, kamar ta Isra’ila, ko da yake masu washewa sun washe su suka kuma lalatar da inabinsu.
For the Lord has turned aside the pride of Jacob, as the pride of Israel: for they have utterly rejected them, and have destroyed their branches.
3 Garkuwoyin sojojinsa ja wur ne; jarumawansa suna sanye da kaya masu ruwan jan garura. Ƙarafan kekunan yaƙi suna walƙiya a ranar da aka shirya su; ana kaɗa māsu da bantsoro.
[They have destroyed] the arms of their power from among men, their mighty men sporting with fire: the reins of their chariots [shall be destroyed] in the day of his preparation, and the horsemen shall be thrown into confusion
4 Kekunan yaƙi sun zabura a tituna, suna kai da kawowa a dandali. Suna walƙiya kamar tocila suna sheƙawa a guje kamar walƙiya.
in the ways, and the chariots shall clash together, and shall be entangled in each other in the broad ways: their appearance is as lamps of fire, and as gleaming lightnings.
5 Ninebe ta tattara rundunarta, duk da haka sun yi ta tuntuɓe a kan hanyarsu. Sun ruga zuwa katangan birnin, sun sanya garkuwar kāriya a inda ya kamata.
And their mighty men shall bethink themselves and flee by day; and they shall be weak as they go; and they shall hasten to her walls, and shall prepare their defences.
6 An buɗe ƙofofin rafuffukan sai wurin ya rurrushe.
The gates of the cities have been opened, and the palaces have fallen into ruin,
7 An umarta cewa birnin za tă tafi bauta, za a kuma yi gaba da su. Bayi’yan mata suna kuka kamar tattabaru suna buga ƙirjinsu.
and the foundation has been exposed; and she has gone up, and her maid-servants were led [away] as doves moaning in their hearts.
8 Ninebe tana kama da tafki, wanda ruwanta yana yoyo. Suna kuka suna cewa, “Ku tsaya! Ku tsaya,” amma ba wanda ya waiga.
And [as for] Nineve, her waters [shall be] as a pool of water: and they fled, and staid not, and there was none to look back.
9 A washe azurfa; a washe zinariya; dukiyarsu ba ta da iyaka, arzikinsu kuma ba ya ƙarewa.
They plundered the silver, they plundered the gold, and there was no end of their adorning; they were loaded [with it] upon all their pleasant vessels.
10 Ta zama wofi, an washe ta, an tuɓe ta! Zukata sun narke, gwiwoyi suna kaɗuwa, jikuna suna rawa, fuskoki duk sun kwantsare!
[There is] thrusting forth, and shaking, and tumult, and heart-breaking, and loosing of knees, and pangs on all loins; and the faces of all [are] as the blackening of a pot.
11 Ina kogon zakokin nan yake yanzu, inda suka ciyar da’ya’yansu, inda zaki da zakanya sukan shiga, da’ya’yansu, ba mai damunsu
Where is the dwelling-place of the lions, and the pasture that belonged to the whelps? where did the lion go, that the lion's whelp should enter in there, and there was none to scare [him] away?
12 Zaki ya kashe abin da ya ishe’ya’yansa ya kuma murɗe wuyan dabbobi ya cika wurin zamansa da abin da ya kama ya cika kogwanninsa da abin da ya kashe.
The lion seized enough prey for his whelps, and strangled for his [young] lions, and filled his lair with prey, and his dwelling-place with spoil.
13 “Ina gāba da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ƙone kekunan yaƙinki, takobi kuma zai fafare’ya’yan zakokinki. Ba kuma zan bar miki namun jejin da za ki kashe a duniya ba. Ba kuwa za a ƙara jin muryar’yan saƙonki ba.”
Behold, I am against thee, saith the Lord Almighty, and I will burn up thy multitude in the smoke, and the sword shall devour thy lions; and I will utterly destroy thy prey from off the land, and thy deeds shall no more at all be heard of.

< Nahum 2 >