< Mika 1 >

1 Maganar Ubangiji ta zo wa Mika mutumin Moreshet a zamanin Yotam, da na Ahaz, da kuma na Hezekiya, sarakunan Yahuda, Mika ya ga wahayi a kan Samariya da kuma a kan Urushalima. Ga abin da ya ce.
La parole de l'Eternel qui fut [adressée] à Michée Morasite au temps de Jotham, Achaz, et Ezéchias, Rois de Juda, laquelle lui [fut adressée] dans une vision, contre Samarie et Jérusalem.
2 Ku ji, ya ku mutane duka, ki saurara, ya ke duniya da dukan mazauna cikinki, bari Ubangiji Mai Iko Duka yă zama shaida a kanku, daga haikalinsa mai tsarki.
Vous tous peuples, écoutez; et toi terre, sois attentive, et que tout ce qui est en elle [écoute]; et que le Seigneur l'Eternel soit témoin contre vous, le Seigneur, [dis-je, sortant] du palais de sa sainteté.
3 Duba! Ubangiji yana zuwa daga wurin zamansa; zai sauko yă taka maɗaukakan wuraren duniya.
Car voici, l'Eternel s'en va sortir de son lieu, il descendra, et marchera sur les lieux hauts de la terre;
4 Duwatsu za su narke a ƙarƙashin ƙafafunsa, kamar kaki a gaban wuta, kwaruruka kuma za su ɓace, kamar ruwan da yake gangarowa daga tsauni.
Et les montagnes se fondront sous lui, et les vallées se fendront, elles seront comme de la cire devant le feu, et comme des eaux qui coulent en une descente.
5 Duk wannan zai faru saboda laifin Yaƙub, da kuma zunuban gidan Isra’ila ne. Mene ne laifin Yaƙub? Shin, ba Samariya ba ce? Ina ne maɗaukakan wuraren Yahuda? Shin, ba Urushalima ba ce?
Tout ceci arrivera à cause du crime de Jacob, et à cause des péchés de la maison d'Israël. [Or] quel est le crime de Jacob? N'est-ce pas Samarie? Et quels sont les hauts lieux de Juda? N'est-ce pas Jérusalem?
6 “Saboda haka zan mai da Samariya tarin juji, wurin noman inabi. Zan zubar da duwatsunta a cikin kwari in kuma bar harsashin gininta a bayyane.
C'est pourquoi je réduirai Samarie [comme] en un monceau de pierres [ramassées] dans les champs [où l'on veut planter des vignes]; et je ferai rouler ses pierres dans la vallée, et je découvrirai ses fondements.
7 Za a ragargaje dukan allolinta; za a ƙone dukan baye-bayenta na haikali da wuta; zan lalatar da dukan gumakanta. Tun da ta wurin karuwanci ne ta tattara su, ga karuwanci kuma za su koma.”
Et toutes ses images taillées seront brisées, tous les salaires de sa prostitution seront brûlés au feu, et je mettrai tous ses faux dieux en désolation; parce qu'elle les a entassés par le moyen du salaire de sa prostitution, ils serviront de salaire à une prostituée.
8 Saboda wannan zan yi baƙin ciki, in yi kuka; zan yi tafiya ba takalmi, zan tuɓe, in kuma yi tafiya tsirara. Zan yi kuka kamar dila, in yi baƙin ciki kamar mujiya.
C'est pourquoi je me plaindrai, et je hurlerai; je m'en irai dépouillé et nu; je ferai une lamentation comme celle des dragons, et je mènerai un deuil comme celui des chats-huants.
9 Gama raunin Samariya ba mai warkewa ba ne; ya bazu har Yahuda. Ya ma kai bakin ƙofar mutanena, har ma Urushalima da kanta.
Car il n'y a pas une de ses plaies qui ne soit incurable, chacune d'elles est venue jusqu'en Juda, et [l'ennemi] est parvenu jusqu'à la porte de mon peuple, jusqu'à Jérusalem.
10 Kada a faɗe shi a Gat; kada ma a yi kuka. A maimako haka, a yi birgima a cikin ƙura a Bet-Leyafra.
Ne l'annoncez point dans Gath, ne pleurez nullement; vautre-toi sur la poussière dans la maison d'Haphra.
11 Ku wuce tsirara da kuma kunya, ku mazaunan Shafir. Bet-Ezel tana makoki domin babu wani daga Za’anan da ya fito don yă taimaka.
Habitante de Saphir passe, ayant ta nudité toute découverte; l'habitante de Tsaanan n'est point sortie pour la complainte de la maison d'Esel; on apprendra de vous à se tenir dans la maison.
12 Mazaunan Marot sun ƙosa su ga alheri, amma Ubangiji ya sauko da azaba, har zuwa ƙofar Urushalima.
Car l'habitante de Maroth aura été dans l'angoisse pour [son] bien; parce que le mal est descendu de par l'Eternel sur la porte de Jérusalem.
13 Ku da kuke zama a Lakish, ku ɗaura wa dawakai kekunan yaƙi. Gama ku kuka fara yin zunubi a Sihiyona, gama an sami laifofin Isra’ila a cikinku.
Attelle le cheval au chariot, habitante de Lakis, [toi qui] es le commencement du péché de la fille de Sion; car en toi ont été trouvés les crimes d'Israël.
14 Saboda haka za ku ba da kyautan bankwana ga Moreshet Gat. Garin Akzib zai zama abin yaudara ga sarakunan Isra’ila.
C'est pourquoi donne des présents à cause de Moreseth de Gath; les maisons d'Aczib mentiront aux Rois d'Israël.
15 Ku mazaunan Maresha Ubangiji zai kawo wanda zai ci ku da yaƙi. Sarakunan Isra’ila za su gudu zuwa Adullam.
Je te ferai aussi venir un héritier, habitante de Maresa; et la gloire d'Israël viendra jusqu'à Hadullam.
16 Ku aske kanku ƙwal don makoki, ku yi wa kanku ƙwalƙwal kamar ungulu. Gama za a ja’ya’yan da kuke farin ciki a kai su bauta.
Arrache tes cheveux, et te fais tondre à cause de tes fils qui font tes délices; arrache tout le poil de ton corps comme un aigle [qui mue], car ils sont emmenés prisonniers [loin] de toi.

< Mika 1 >