< Mika 1 >

1 Maganar Ubangiji ta zo wa Mika mutumin Moreshet a zamanin Yotam, da na Ahaz, da kuma na Hezekiya, sarakunan Yahuda, Mika ya ga wahayi a kan Samariya da kuma a kan Urushalima. Ga abin da ya ce.
La parole de l’Éternel qui vint à Michée, le Morashtite, aux jours de Jotham, d’Achaz, d’Ézéchias, rois de Juda, laquelle il vit au sujet de Samarie et de Jérusalem.
2 Ku ji, ya ku mutane duka, ki saurara, ya ke duniya da dukan mazauna cikinki, bari Ubangiji Mai Iko Duka yă zama shaida a kanku, daga haikalinsa mai tsarki.
Écoutez, vous, tous les peuples; sois attentive, terre, et tout ce qui est en toi; et que le Seigneur, l’Éternel, soit témoin contre vous, le Seigneur, du palais de sa sainteté!
3 Duba! Ubangiji yana zuwa daga wurin zamansa; zai sauko yă taka maɗaukakan wuraren duniya.
Car voici, l’Éternel sort de son lieu, et descendra, et marchera sur les lieux hauts de la terre;
4 Duwatsu za su narke a ƙarƙashin ƙafafunsa, kamar kaki a gaban wuta, kwaruruka kuma za su ɓace, kamar ruwan da yake gangarowa daga tsauni.
et les montagnes se fondront sous lui, et les vallées s’entrouvriront, comme la cire devant le feu, comme des eaux versées sur une pente.
5 Duk wannan zai faru saboda laifin Yaƙub, da kuma zunuban gidan Isra’ila ne. Mene ne laifin Yaƙub? Shin, ba Samariya ba ce? Ina ne maɗaukakan wuraren Yahuda? Shin, ba Urushalima ba ce?
Tout cela, à cause de la transgression de Jacob et à cause des péchés de la maison d’Israël! [De] qui est la transgression de Jacob? N’est-ce pas [de] Samarie? Et [de] qui, les hauts lieux de Juda? N’est-ce pas [de] Jérusalem?
6 “Saboda haka zan mai da Samariya tarin juji, wurin noman inabi. Zan zubar da duwatsunta a cikin kwari in kuma bar harsashin gininta a bayyane.
Et je ferai de Samarie un monceau dans les champs, des plantations de vigne; et je ferai rouler ses pierres dans la vallée, et je découvrirai ses fondements.
7 Za a ragargaje dukan allolinta; za a ƙone dukan baye-bayenta na haikali da wuta; zan lalatar da dukan gumakanta. Tun da ta wurin karuwanci ne ta tattara su, ga karuwanci kuma za su koma.”
Et toutes ses images taillées seront mises en pièces; et tous ses présents [de prostitution] seront brûlés au feu; et je mettrai en désolation toutes ses idoles; car c’est avec un présent de prostituée qu’elle les a rassemblées, et elles redeviendront un présent de prostituée.
8 Saboda wannan zan yi baƙin ciki, in yi kuka; zan yi tafiya ba takalmi, zan tuɓe, in kuma yi tafiya tsirara. Zan yi kuka kamar dila, in yi baƙin ciki kamar mujiya.
À cause de cela je me frapperai [la poitrine], et je hurlerai; j’irai dépouillé et nu; je ferai une lamentation comme les chacals, et des cris de deuil comme les autruches.
9 Gama raunin Samariya ba mai warkewa ba ne; ya bazu har Yahuda. Ya ma kai bakin ƙofar mutanena, har ma Urushalima da kanta.
Car sa plaie est incurable; car elle est venue jusqu’à Juda, elle atteint jusqu’à la porte de mon peuple, jusqu’à Jérusalem.
10 Kada a faɗe shi a Gat; kada ma a yi kuka. A maimako haka, a yi birgima a cikin ƙura a Bet-Leyafra.
Ne le racontez pas dans Gath, ne versez point de pleurs. Dans Beth-Leaphra, roule-toi dans la poussière.
11 Ku wuce tsirara da kuma kunya, ku mazaunan Shafir. Bet-Ezel tana makoki domin babu wani daga Za’anan da ya fito don yă taimaka.
Passe outre, toi, habitante de Shaphir, ta nudité découverte! L’habitante de Tsaanan n’est pas sortie [pour] la lamentation de Beth-Haëtsel; il vous ôtera son abri.
12 Mazaunan Marot sun ƙosa su ga alheri, amma Ubangiji ya sauko da azaba, har zuwa ƙofar Urushalima.
Car l’habitante de Maroth s’attendait au bien, mais le mal est descendu de par l’Éternel à la porte de Jérusalem.
13 Ku da kuke zama a Lakish, ku ɗaura wa dawakai kekunan yaƙi. Gama ku kuka fara yin zunubi a Sihiyona, gama an sami laifofin Isra’ila a cikinku.
Attache le char au coursier, habitante de Lakis: elle a été les prémices du péché pour la fille de Sion; car en toi ont été trouvées les transgressions d’Israël.
14 Saboda haka za ku ba da kyautan bankwana ga Moreshet Gat. Garin Akzib zai zama abin yaudara ga sarakunan Isra’ila.
C’est pourquoi tu donneras des présents à Morésheth-Gath. Les maisons d’Aczib seront un mensonge pour les rois d’Israël.
15 Ku mazaunan Maresha Ubangiji zai kawo wanda zai ci ku da yaƙi. Sarakunan Isra’ila za su gudu zuwa Adullam.
À toi j’amènerai encore l’héritier, habitante de Marésha; la gloire d’Israël viendra jusqu’à Adullam.
16 Ku aske kanku ƙwal don makoki, ku yi wa kanku ƙwalƙwal kamar ungulu. Gama za a ja’ya’yan da kuke farin ciki a kai su bauta.
Rends-toi chauve et coupe tes cheveux pour les fils de tes délices; élargis ta tonsure, comme le vautour; car ils sont allés en captivité loin de toi.

< Mika 1 >