< Mika 1 >

1 Maganar Ubangiji ta zo wa Mika mutumin Moreshet a zamanin Yotam, da na Ahaz, da kuma na Hezekiya, sarakunan Yahuda, Mika ya ga wahayi a kan Samariya da kuma a kan Urushalima. Ga abin da ya ce.
[I am] Micah. I am from [the town of] Moresheth [in Judah]. Yahweh gave me these [messages in] visions about Samaria and Jerusalem during the time when Jotham, [and then] Ahaz, and [then] Hezekiah, were the kings of Judah.
2 Ku ji, ya ku mutane duka, ki saurara, ya ke duniya da dukan mazauna cikinki, bari Ubangiji Mai Iko Duka yă zama shaida a kanku, daga haikalinsa mai tsarki.
You people everywhere on the earth, pay attention to this [DOU]! Yahweh our God is accusing you from his holy temple [in heaven].
3 Duba! Ubangiji yana zuwa daga wurin zamansa; zai sauko yă taka maɗaukakan wuraren duniya.
He will come down [from heaven] and walk on the tops of the highest mountains.
4 Duwatsu za su narke a ƙarƙashin ƙafafunsa, kamar kaki a gaban wuta, kwaruruka kuma za su ɓace, kamar ruwan da yake gangarowa daga tsauni.
[It will be as though] the mountains will melt under his [feet] like [SIM] wax [melts] in front of a fire, and like [SIM] water [disappears] when it rushes/flows down into a valley.
5 Duk wannan zai faru saboda laifin Yaƙub, da kuma zunuban gidan Isra’ila ne. Mene ne laifin Yaƙub? Shin, ba Samariya ba ce? Ina ne maɗaukakan wuraren Yahuda? Shin, ba Urushalima ba ce?
Those things will happen because of the terrible sins [DOU] that the people [MTY] of Israel, [the descendants of] Jacob, have committed. But it was [RHQ] [the people of] Samaria [city who persuaded all the people of] Israel to sin, and it was [RHQ] because the people of Jerusalem [set up altars to worship their gods] that [the other people of] Judah [were persuaded to worship idols on] their hilltops.
6 “Saboda haka zan mai da Samariya tarin juji, wurin noman inabi. Zan zubar da duwatsunta a cikin kwari in kuma bar harsashin gininta a bayyane.
So Yahweh will cause Samaria to become a heap [of rubble/ruins]; [it will be only] a field for planting vineyards. He will cause the stones of its [buildings] to roll down into the valley, and the foundations [of the buildings] will be uncovered.
7 Za a ragargaje dukan allolinta; za a ƙone dukan baye-bayenta na haikali da wuta; zan lalatar da dukan gumakanta. Tun da ta wurin karuwanci ne ta tattara su, ga karuwanci kuma za su koma.”
All the idols in Samaria will be smashed, and the gifts [given to prostitutes at the temples of their idols] will be destroyed in a fire. And because people paid prostitutes there, [their enemies will take away those idols and sell them] to get money to pay to prostitutes [in other countries].
8 Saboda wannan zan yi baƙin ciki, in yi kuka; zan yi tafiya ba takalmi, zan tuɓe, in kuma yi tafiya tsirara. Zan yi kuka kamar dila, in yi baƙin ciki kamar mujiya.
Because [Samaria will be destroyed], I will weep and wail. I will walk around (barefoot/without any sandals on my feet) and naked. I will howl like a jackal/wolf and screech like an owl,
9 Gama raunin Samariya ba mai warkewa ba ne; ya bazu har Yahuda. Ya ma kai bakin ƙofar mutanena, har ma Urushalima da kanta.
because Samaria will be completely destroyed [MET]; nothing can save that city. But the same thing will happen to Judah! [It is as though the enemy army] has [already] reached the city gates of Jerusalem, [the main city where] my people [live].
10 Kada a faɗe shi a Gat; kada ma a yi kuka. A maimako haka, a yi birgima a cikin ƙura a Bet-Leyafra.
Do not tell that to [our enemies] in Gath [city in Philistia]! Do not cry, [lest the people there find out what is happening]! [Instead, just] roll in the dirt in Beth-Leaphrah [because the name of that town means ‘house of dust].’
11 Ku wuce tsirara da kuma kunya, ku mazaunan Shafir. Bet-Ezel tana makoki domin babu wani daga Za’anan da ya fito don yă taimaka.
You people who live in Shaphir [town, whose name means ‘beautiful],’ naked and ashamed, you will be taken [to another country]. [You people in] Beth-Ezel [town] should mourn, [because] no one from Zaanan [town, whose name means ‘one who goes out],’ will go out to help you.
12 Mazaunan Marot sun ƙosa su ga alheri, amma Ubangiji ya sauko da azaba, har zuwa ƙofar Urushalima.
[The name of] Maroth [town sounds like ‘bitterness];’ everyone there is anxiously waiting for good things to happen to them, but good things will not happen to them; instead, terrible things are about to happen to them, and it will soon happen at the gates of Jerusalem.
13 Ku da kuke zama a Lakish, ku ɗaura wa dawakai kekunan yaƙi. Gama ku kuka fara yin zunubi a Sihiyona, gama an sami laifofin Isra’ila a cikinku.
You people of Lachish [city, whose name sounds like ‘team],’ hitch your horses to pull the chariots [in which you can ride to flee from your enemies]. The Israeli people rebelled against Yahweh, and you (imitated them/did the same evil things that they did), and that caused the people of Jerusalem [IDM] to start sinning, too.
14 Saboda haka za ku ba da kyautan bankwana ga Moreshet Gat. Garin Akzib zai zama abin yaudara ga sarakunan Isra’ila.
[You people of Judah], send a farewell gift to [the people] of Moresheth [town], [because their enemies will soon destroy it]. [The name of the town Aczib means ‘deception],’ and the kings of Israel [will soon find out that the people of that town] will deceive them.
15 Ku mazaunan Maresha Ubangiji zai kawo wanda zai ci ku da yaƙi. Sarakunan Isra’ila za su gudu zuwa Adullam.
[The name of your town of] Mareshah [means ‘conqueror],’ and Yahweh will [soon] send someone to conquer your town. [It will be necessary for] the great/glorious leaders of Israel to go [and hide in the cave at] Adullam [city].
16 Ku aske kanku ƙwal don makoki, ku yi wa kanku ƙwalƙwal kamar ungulu. Gama za a ja’ya’yan da kuke farin ciki a kai su bauta.
[You people of Judah], shave your heads [while you will be mourning], because your children whom you love will [soon] be (exiled/forced to leave you and go to another country).

< Mika 1 >