< Mika 7 >
1 Tawa ta ƙare! Ina kama da wanda yake tattara’ya’yan itatuwa a lokacin kalar’ya’yan inabi; babu sauran nonon inabin da za a tsinka a ci, babu kuma’ya’yan ɓaure na farko-farkon da raina yake marmari.
Malheur à moi, parce que je suis devenu comme celui qui recueille en automne des grappes de raisins oubliées pendant la vendange; il n’y a pas une grappe à manger; mon âme a désiré quelques figues précoces.
2 An kawar da masu tsoron Allah daga ƙasar; babu sauran mai adalcin da ya rage. Dukan mutane suna kwanto don su zub da jini; kowa yana farautar ɗan’uwansa da tarko.
Le saint a disparu de la terre, il n’y a pas un juste parmi les hommes; tous tendent des pièges dans le sang; l’homme fait une chasse à mort à son frère.
3 Dukan hannuwansu sun gwaninta wajen yin mugunta; shugabanni suna nema a ba su kyautai, alƙalai suna nema a ba su cin hanci, masu iko suna faɗar son zuciyarsu, duk suna ƙulla makirci tare.
Ils appellent bien le mal de leurs mains; le prince demande, et le juge est pour la rétribution, et le grand a dit le désir de son âme, et ainsi ils ont troublé la terre.
4 Mafi kyau a cikinsu yana kama da ƙaya, mafi gaskiyarsu ya fi shingen ƙaya muni. Ranar da Allah zai ziyarce ku ta zo, ranar da masu gadinku za su hura ƙaho. Yanzu ne lokacin ruɗewarku.
Celui qui est le meilleur d’entre eux est comme un paliure, et celui qui est juste, comme l’épine d’une haie. Le jour de ton inspection, ta visite est venue; alors sera leur désolation.
5 Kada ka yarda da maƙwabci; kada ka sa begenka ga abokai. Ko ma wadda take kwance a ƙirjinka, ka yi hankali da kalmominka.
Ne croyez pas à un ami, et ne vous confiez pas à un guide; pour celle qui dort près de toi, ferme la porte de ta bouche.
6 Gama ɗa yakan ce wannan ba mahaifinsa ba ne, diya kuma takan tayar wa mahaifiyarta, matar ɗa takan yi gāba da uwar mijinta, abokan gāban mutum su ne iyalin cikin gidansa.
Le fils fait outrage à son père, et la fille s’élève contre sa mère, la belle-fille contre sa belle-mère; les ennemis de l’homme sont ses serviteurs.
7 Amma game da ni, zan sa bege ga Ubangiji, ina sauraron Allah Mai Cetona; Allahna kuwa zai ji ni.
Mais moi, je porterai mes regards sur le Seigneur, j’attendrai le Dieu mon Sauveur; mon Dieu m’écoutera.
8 Kada ku yi farin ciki, ku maƙiyana! Ko da yake na fāɗi, zan tashi. Ko da yake na zauna a cikin duhu, Ubangiji zai zama haskena.
Ne te réjouis pas sur moi, mon ennemie, parce que je suis tombée; je me relèverai lorsque je me serai assise dans les ténèbres, le Seigneur est ma lumière.
9 Domin na yi masa zunubi, zan fuskanci fushin Ubangiji, har sai ya dubi batuna ya kuma tabbatar da’yancina. Zai kawo ni zuwa wurin haske; zan ga adalcinsa.
Je porterai la colère du Seigneur, parce que j’ai péché contre lui, jusqu’à ce qu’il juge ma cause et qu’il accomplisse mon jugement: il me fera sortir à la lumière, je verrai sa justice.
10 Sa’an nan maƙiyina zai gani yă kuma sha kunya, shi da yake ce da ni “Ina Ubangiji Allahnka?” Zai gani, yă kuma ji kunya. Ko yanzu ma za a tattake shi kamar taɓo a tituna.
Et mon ennemie verra et sera couverte de confusion, elle qui me dit: Où est le Seigneur ton Dieu? Mes yeux la verront; alors elle sera foulée aux pieds comme la boue des places publiques.
11 Ranar gina katangarka tana zuwa, a ranar za a fadada iyakokinka.
Le jour où les murs de clôture seront bâtis, en ce jour-là s’éloignera de toi la loi.
12 A wannan rana mutane za su zo gare ka daga Assuriya da kuma biranen Masar, daga Masar ma har zuwa Yuferites daga teku zuwa teku, kuma daga dutse zuwa dutse.
En ce jour-là, on viendra d’Assur et jusqu’à toi et jusqu’à tes cités fortifiées; et des cités fortifiées jusqu’au fleuve, et d’une mer à l’autre mer, et de la montagne jusqu’à la montagne.
13 Duniya za tă zama kufai saboda mazaunanta, saboda ayyukansu.
Et la terre sera désolée à cause de ses habitants et à cause du fruit de leurs pensées.
14 Ka yi kiwon mutanenka da sandarka, garken gādonka, wanda yake zaune shi kaɗai a kurmi, a ƙasa mai kyau ta kiwo, bari su yi kiwo a Bashan da Gileyad kamar a kwanakin dā.
Seigneur, paissez avec votre verge votre peuple, le troupeau de votre héritage, qui demeure seul dans la forêt, au milieu du Carmel; ils paîtront en Basan et en Galaad, comme aux jours anciens.
15 “Kamar a kwanakin da kuka fito daga Masar, zan nuna musu al’ajabaina.”
Comme aux jours de ta sortie de la terre d’Egypte, je lui ferai voir des merveilles.
16 Al’ummai za su gani su kuma ji kunya, za a kuma ƙwace musu dukan ikonsu. Za su kama bakinsu kunnuwansu kuma za su zama kurame.
Des nations verront, et seront confondues avec toute leur puissance; elles mettront la main sur leur bouche, et leurs oreilles seront assourdies.
17 Za su lashi ƙura kamar maciji, kamar dabbobi masu rarrafe a ƙasa. Za su fito daga maɓuyarsu da rawan jiki, za su juya cikin tsoro ga Ubangiji Allahnmu su kuma ji tsoronku.
Elles lécheront la poussière comme les serpents; comme les reptiles de la terre, elles seront fortement troublées dans leurs demeures; elles redouteront le Seigneur notre Dieu, et elles te craindront, ô Israël.
18 Wane ne Allah kamar ka, wanda yake yafe zunubi yă kuma gafarta laifofin mutanensa da suka ragu? Ba ka zama mai fushi har abada amma kana marmari ka nuna jinƙai.
Quel Dieu est semblable à vous, qui ôtez l’iniquité, et passez sous silence le péché du reste de votre héritage? il n’enverra plus désormais sa fureur, parce qu’il veut la miséricorde.
19 Za ka sāke jin tausayinmu; za ka tattake zunubanmu a ƙarƙashin sawunka ka kuma tura dukan kurakuranmu zuwa cikin zurfafan teku.
Il reviendra, et il aura pitié de nous; il laissera de côté nos iniquités, et il jettera dans le profond de la mer tous nos péchés.
20 Za ka yi wa Yaƙub aminci, ka kuma nuna jinƙai ga Ibrahim, kamar yadda ka yi alkawari da rantsuwa ga kakanninmu tun a kwanankin dā.
Seigneur, vous accomplirez votre vérité envers Jacob, votre miséricorde envers Abraham; ce que vous avez juré à nos pères dès les jours anciens.