< Mika 7 >
1 Tawa ta ƙare! Ina kama da wanda yake tattara’ya’yan itatuwa a lokacin kalar’ya’yan inabi; babu sauran nonon inabin da za a tsinka a ci, babu kuma’ya’yan ɓaure na farko-farkon da raina yake marmari.
I'm totally miserable! I've become like someone trying to glean summer fruit after the grape harvest is over. I can't find any grapes to eat, and there are no early figs that I love.
2 An kawar da masu tsoron Allah daga ƙasar; babu sauran mai adalcin da ya rage. Dukan mutane suna kwanto don su zub da jini; kowa yana farautar ɗan’uwansa da tarko.
All the good people in the country are gone, there's no one who does right left anywhere. Everyone is looking to murder others; they try to trap even their own brothers.
3 Dukan hannuwansu sun gwaninta wajen yin mugunta; shugabanni suna nema a ba su kyautai, alƙalai suna nema a ba su cin hanci, masu iko suna faɗar son zuciyarsu, duk suna ƙulla makirci tare.
They are experts at evil; both officials and judges ask for bribes; the powerful demand their evil desires; and they scheme together to get what they want.
4 Mafi kyau a cikinsu yana kama da ƙaya, mafi gaskiyarsu ya fi shingen ƙaya muni. Ranar da Allah zai ziyarce ku ta zo, ranar da masu gadinku za su hura ƙaho. Yanzu ne lokacin ruɗewarku.
Even the best of them is like a thorny bush, the most honest like a thorn hedge. Your day of judgment that was announced by the prophets, your time of punishment, has arrived. You'rethrown into complete confusion.
5 Kada ka yarda da maƙwabci; kada ka sa begenka ga abokai. Ko ma wadda take kwance a ƙirjinka, ka yi hankali da kalmominka.
Don't trust a neighbor, don't rely on a friend. Watch what you say even to the one who lies in your arms.
6 Gama ɗa yakan ce wannan ba mahaifinsa ba ne, diya kuma takan tayar wa mahaifiyarta, matar ɗa takan yi gāba da uwar mijinta, abokan gāban mutum su ne iyalin cikin gidansa.
For a son treats his father with contempt; a daughter opposes her mother, and a daughter-in-law her mother-in-law. Your enemies are members of your own family.
7 Amma game da ni, zan sa bege ga Ubangiji, ina sauraron Allah Mai Cetona; Allahna kuwa zai ji ni.
But as for me, I look to the Lord. I will wait for the God who saves me. My God will hear me.
8 Kada ku yi farin ciki, ku maƙiyana! Ko da yake na fāɗi, zan tashi. Ko da yake na zauna a cikin duhu, Ubangiji zai zama haskena.
Don't gloat over me, my enemies! Even though I fall, I will rise again. Though I sit in darkness, the Lord is my light.
9 Domin na yi masa zunubi, zan fuskanci fushin Ubangiji, har sai ya dubi batuna ya kuma tabbatar da’yancina. Zai kawo ni zuwa wurin haske; zan ga adalcinsa.
I will endure the Lord's anger because I have sinned against him. But after that he will argue my case and give me justice. He will bring me into the light and I will see his integrity.
10 Sa’an nan maƙiyina zai gani yă kuma sha kunya, shi da yake ce da ni “Ina Ubangiji Allahnka?” Zai gani, yă kuma ji kunya. Ko yanzu ma za a tattake shi kamar taɓo a tituna.
Then my enemies will see it and cover their faces in shame for taunting me, asking, “Where is the Lord your God?” With my own eyes I will see what happens to them; they will be trodden down like mud in the streets.
11 Ranar gina katangarka tana zuwa, a ranar za a fadada iyakokinka.
On that day it will be time to build your walls. On that day your boundaries will be extended.
12 A wannan rana mutane za su zo gare ka daga Assuriya da kuma biranen Masar, daga Masar ma har zuwa Yuferites daga teku zuwa teku, kuma daga dutse zuwa dutse.
On that day people will come from Assyria and the cities of Egypt, from Egypt to the Euphrates River, from sea to sea, from mountain to mountain.
13 Duniya za tă zama kufai saboda mazaunanta, saboda ayyukansu.
But the rest of the earth will become desolate because of what those who live there have done.
14 Ka yi kiwon mutanenka da sandarka, garken gādonka, wanda yake zaune shi kaɗai a kurmi, a ƙasa mai kyau ta kiwo, bari su yi kiwo a Bashan da Gileyad kamar a kwanakin dā.
Protect your people with your shepherd's rod. Take care of your flock, your special people, who live alone in the wilderness and in cultivated land. Let them feed in Basham and Gilead as they did long ago.
15 “Kamar a kwanakin da kuka fito daga Masar, zan nuna musu al’ajabaina.”
Like the time when you left the land of Egypt, I will do miracles for you.
16 Al’ummai za su gani su kuma ji kunya, za a kuma ƙwace musu dukan ikonsu. Za su kama bakinsu kunnuwansu kuma za su zama kurame.
The nations will see, and they will be humiliated despite their strength. They will cover their mouths with their hands, and their ears shall become deaf.
17 Za su lashi ƙura kamar maciji, kamar dabbobi masu rarrafe a ƙasa. Za su fito daga maɓuyarsu da rawan jiki, za su juya cikin tsoro ga Ubangiji Allahnmu su kuma ji tsoronku.
They will lick the dust like snakes; they will be like the creepy-crawlies of the earth. They will come trembling from their fortresses to meet the Lord our God, fearful and afraid before him.
18 Wane ne Allah kamar ka, wanda yake yafe zunubi yă kuma gafarta laifofin mutanensa da suka ragu? Ba ka zama mai fushi har abada amma kana marmari ka nuna jinƙai.
Who is a God like you who forgives sin and passes over the rebellion of those who are left of his special people? You do not remain angry forever because you delight in showing faithful love.
19 Za ka sāke jin tausayinmu; za ka tattake zunubanmu a ƙarƙashin sawunka ka kuma tura dukan kurakuranmu zuwa cikin zurfafan teku.
You will have compassion on us again. You will tread our sins under your feet, and you will throw our sins into the depths of the sea.
20 Za ka yi wa Yaƙub aminci, ka kuma nuna jinƙai ga Ibrahim, kamar yadda ka yi alkawari da rantsuwa ga kakanninmu tun a kwanankin dā.
You will give your trustworthy truth to the people of Jacob, your faithful love to the people of Abraham, as you promised our forefathers long ago.