< Mika 7 >

1 Tawa ta ƙare! Ina kama da wanda yake tattara’ya’yan itatuwa a lokacin kalar’ya’yan inabi; babu sauran nonon inabin da za a tsinka a ci, babu kuma’ya’yan ɓaure na farko-farkon da raina yake marmari.
Woe to me, for I have become just like one who gleans the clusters of the vintage in autumn. There is no cluster of grapes to consume; my soul desired figs out of season.
2 An kawar da masu tsoron Allah daga ƙasar; babu sauran mai adalcin da ya rage. Dukan mutane suna kwanto don su zub da jini; kowa yana farautar ɗan’uwansa da tarko.
The holy ones pass away from the land, and there is no one righteous among men. All wait in ambush for blood; a man hunts his brother to death.
3 Dukan hannuwansu sun gwaninta wajen yin mugunta; shugabanni suna nema a ba su kyautai, alƙalai suna nema a ba su cin hanci, masu iko suna faɗar son zuciyarsu, duk suna ƙulla makirci tare.
The evil of their hands, they call good. The leader is demanding, and the judge is yielding, and the great is speaking the desire of his soul, and they have confused it.
4 Mafi kyau a cikinsu yana kama da ƙaya, mafi gaskiyarsu ya fi shingen ƙaya muni. Ranar da Allah zai ziyarce ku ta zo, ranar da masu gadinku za su hura ƙaho. Yanzu ne lokacin ruɗewarku.
Whoever is best among them is like a thorny plant, and he who is righteous is like a thorny hedge. The day of your inspection, your visitation, arrives. Now will be their ruination.
5 Kada ka yarda da maƙwabci; kada ka sa begenka ga abokai. Ko ma wadda take kwance a ƙirjinka, ka yi hankali da kalmominka.
Do not be willing to believe a friend. And do not be willing to confide in a commander. From her, who sleeps in your bosom, keep the doors of your mouth closed.
6 Gama ɗa yakan ce wannan ba mahaifinsa ba ne, diya kuma takan tayar wa mahaifiyarta, matar ɗa takan yi gāba da uwar mijinta, abokan gāban mutum su ne iyalin cikin gidansa.
For the son acts with contempt for the father, and the daughter rises up against her mother, the daughter-in-law against her mother-in-law, and a man’s enemies are those of his own household.
7 Amma game da ni, zan sa bege ga Ubangiji, ina sauraron Allah Mai Cetona; Allahna kuwa zai ji ni.
But I will look towards the Lord. I will wait for God, my Savior. My God will hear me.
8 Kada ku yi farin ciki, ku maƙiyana! Ko da yake na fāɗi, zan tashi. Ko da yake na zauna a cikin duhu, Ubangiji zai zama haskena.
You, my enemy, should not rejoice over me because I have fallen. I will rise up, when I sit in darkness. The Lord is my light.
9 Domin na yi masa zunubi, zan fuskanci fushin Ubangiji, har sai ya dubi batuna ya kuma tabbatar da’yancina. Zai kawo ni zuwa wurin haske; zan ga adalcinsa.
I will carry the wrath of the Lord, because I have sinned against him, until he may judge my case and execute judgment for me. He will lead me into the light. I will behold his justice.
10 Sa’an nan maƙiyina zai gani yă kuma sha kunya, shi da yake ce da ni “Ina Ubangiji Allahnka?” Zai gani, yă kuma ji kunya. Ko yanzu ma za a tattake shi kamar taɓo a tituna.
And my enemy will look, and she will be covered with confusion, she who says to me, “Where is the Lord your God?” My eyes will look upon her. Now she will be trampled underfoot like the mud of the streets.
11 Ranar gina katangarka tana zuwa, a ranar za a fadada iyakokinka.
The day that your walls will be rebuilt, in that day the law will be far away.
12 A wannan rana mutane za su zo gare ka daga Assuriya da kuma biranen Masar, daga Masar ma har zuwa Yuferites daga teku zuwa teku, kuma daga dutse zuwa dutse.
In that day also, they will come towards you even from Assur, and even to the fortified cities, and from the fortified cities even to the river, and from sea to sea, and from mountain to mountain.
13 Duniya za tă zama kufai saboda mazaunanta, saboda ayyukansu.
And the land will be in desolation, because of its inhabitants and because of the fruit of their intentions.
14 Ka yi kiwon mutanenka da sandarka, garken gādonka, wanda yake zaune shi kaɗai a kurmi, a ƙasa mai kyau ta kiwo, bari su yi kiwo a Bashan da Gileyad kamar a kwanakin dā.
With your rod, pasture your people, the flock of your inheritance, living alone in the narrow forest, in the midst of Carmel. They will graze in Bashan and Gilead, as in the ancient days.
15 “Kamar a kwanakin da kuka fito daga Masar, zan nuna musu al’ajabaina.”
As in the days of your departure from the land of Egypt, I will reveal miracles to him.
16 Al’ummai za su gani su kuma ji kunya, za a kuma ƙwace musu dukan ikonsu. Za su kama bakinsu kunnuwansu kuma za su zama kurame.
The nations will look, and they will be confounded at the strength of them all. They will place hand over mouth; their ears will be deaf.
17 Za su lashi ƙura kamar maciji, kamar dabbobi masu rarrafe a ƙasa. Za su fito daga maɓuyarsu da rawan jiki, za su juya cikin tsoro ga Ubangiji Allahnmu su kuma ji tsoronku.
They will lick the dust like serpents, and, like the creeping things of the earth, they will be disturbed in their houses. They will dread the Lord our God, and they will fear you.
18 Wane ne Allah kamar ka, wanda yake yafe zunubi yă kuma gafarta laifofin mutanensa da suka ragu? Ba ka zama mai fushi har abada amma kana marmari ka nuna jinƙai.
What God is like you, who takes away iniquity and passes over the sin of the remnant of your inheritance? No longer will he send forth his fury, because he is willing to be merciful.
19 Za ka sāke jin tausayinmu; za ka tattake zunubanmu a ƙarƙashin sawunka ka kuma tura dukan kurakuranmu zuwa cikin zurfafan teku.
He will turn back and have mercy on us. He will put away our iniquities, and he will cast all our sins into the depths of the sea.
20 Za ka yi wa Yaƙub aminci, ka kuma nuna jinƙai ga Ibrahim, kamar yadda ka yi alkawari da rantsuwa ga kakanninmu tun a kwanankin dā.
You will give the truth to Jacob, mercy to Abraham, which you swore to our fathers from the ancient days.

< Mika 7 >