< Mika 7 >
1 Tawa ta ƙare! Ina kama da wanda yake tattara’ya’yan itatuwa a lokacin kalar’ya’yan inabi; babu sauran nonon inabin da za a tsinka a ci, babu kuma’ya’yan ɓaure na farko-farkon da raina yake marmari.
Alas for me! for I am become as one gathering straw in harvest, and as [one gathering] grape-gleanings in the vintage, when there is no cluster for me to eat the first-ripe fruit: alas my soul!
2 An kawar da masu tsoron Allah daga ƙasar; babu sauran mai adalcin da ya rage. Dukan mutane suna kwanto don su zub da jini; kowa yana farautar ɗan’uwansa da tarko.
For the godly is perished from the earth; and there is none among men that orders [his way] aright: they all quarrel even to blood: they grievously afflict every one his neighbour:
3 Dukan hannuwansu sun gwaninta wajen yin mugunta; shugabanni suna nema a ba su kyautai, alƙalai suna nema a ba su cin hanci, masu iko suna faɗar son zuciyarsu, duk suna ƙulla makirci tare.
they prepare their hands for mischief, the prince asks [a reward], and the judge speaks flattering words; it is the desire of their soul:
4 Mafi kyau a cikinsu yana kama da ƙaya, mafi gaskiyarsu ya fi shingen ƙaya muni. Ranar da Allah zai ziyarce ku ta zo, ranar da masu gadinku za su hura ƙaho. Yanzu ne lokacin ruɗewarku.
therefore I will take away their goods as a devouring moth, and as one who acts by a [rigid] rule in a day of visitation. Woe, woe, thy times of vengeance are come; now shall be their lamentations.
5 Kada ka yarda da maƙwabci; kada ka sa begenka ga abokai. Ko ma wadda take kwance a ƙirjinka, ka yi hankali da kalmominka.
Trust not in friends, and confide not in guides: beware of thy wife, so as not to commit anything to her.
6 Gama ɗa yakan ce wannan ba mahaifinsa ba ne, diya kuma takan tayar wa mahaifiyarta, matar ɗa takan yi gāba da uwar mijinta, abokan gāban mutum su ne iyalin cikin gidansa.
For the son dishonours his father, the daughter will rise up against her mother, the daughter-in-law against her mother-in-law: those in his house [shall be] all a man's enemies.
7 Amma game da ni, zan sa bege ga Ubangiji, ina sauraron Allah Mai Cetona; Allahna kuwa zai ji ni.
But I will look to the Lord; I will wait upon God my Saviour: my God will hearken to me.
8 Kada ku yi farin ciki, ku maƙiyana! Ko da yake na fāɗi, zan tashi. Ko da yake na zauna a cikin duhu, Ubangiji zai zama haskena.
Rejoice not against me, mine enemy; for I have fallen [yet] shall arise; for though I should sit in darkness, the Lord shall be a light to me.
9 Domin na yi masa zunubi, zan fuskanci fushin Ubangiji, har sai ya dubi batuna ya kuma tabbatar da’yancina. Zai kawo ni zuwa wurin haske; zan ga adalcinsa.
I will bear the indignation of the Lord, because I have sinned against him, until he make good my cause: he also shall maintain my right, and shall bring me out to the light, [and] I shall behold his righteousness.
10 Sa’an nan maƙiyina zai gani yă kuma sha kunya, shi da yake ce da ni “Ina Ubangiji Allahnka?” Zai gani, yă kuma ji kunya. Ko yanzu ma za a tattake shi kamar taɓo a tituna.
And she that is mine enemy shall see it, and shall clothe herself with shame, who says, Where [is] the Lord thy God? mine eyes shall look upon her: now shall she be for trampling as mire in the ways.
11 Ranar gina katangarka tana zuwa, a ranar za a fadada iyakokinka.
[It is] the day of making of brick; that day shall be thine utter destruction, and that day shall utterly abolish thine ordinances.
12 A wannan rana mutane za su zo gare ka daga Assuriya da kuma biranen Masar, daga Masar ma har zuwa Yuferites daga teku zuwa teku, kuma daga dutse zuwa dutse.
And thy cities shall be levelled, and parted among the Assyrians; and thy strong cities shall be parted from Tyre to the river, and from sea to sea, and from mountain to mountain.
13 Duniya za tă zama kufai saboda mazaunanta, saboda ayyukansu.
And the land shall be utterly desolate together with them that inhabit it, because of the fruit of their doings.
14 Ka yi kiwon mutanenka da sandarka, garken gādonka, wanda yake zaune shi kaɗai a kurmi, a ƙasa mai kyau ta kiwo, bari su yi kiwo a Bashan da Gileyad kamar a kwanakin dā.
Tend thy people with thy rod, the sheep of thine inheritance, those that inhabit by themselves the thicket in the midst of Carmel: they shall feed in the land of Basan, and in the land of Galaad, as in the days of old.
15 “Kamar a kwanakin da kuka fito daga Masar, zan nuna musu al’ajabaina.”
And according to the days of thy departure out of Egypt shall ye see marvellous [things].
16 Al’ummai za su gani su kuma ji kunya, za a kuma ƙwace musu dukan ikonsu. Za su kama bakinsu kunnuwansu kuma za su zama kurame.
The nations shall see and be ashamed; and at all their might they shall lay their hands upon their mouth, their ears shall be deafened.
17 Za su lashi ƙura kamar maciji, kamar dabbobi masu rarrafe a ƙasa. Za su fito daga maɓuyarsu da rawan jiki, za su juya cikin tsoro ga Ubangiji Allahnmu su kuma ji tsoronku.
They shall lick the dust as serpents crawling on the earth, they shall be confounded in their holes; they shall be amazed at the Lord our God, and will be afraid of thee.
18 Wane ne Allah kamar ka, wanda yake yafe zunubi yă kuma gafarta laifofin mutanensa da suka ragu? Ba ka zama mai fushi har abada amma kana marmari ka nuna jinƙai.
Who is a God like thee, cancelling iniquities, and passing over the sins of the remnant of his inheritance? and he has not kept his anger for a testimony, for he delights in mercy.
19 Za ka sāke jin tausayinmu; za ka tattake zunubanmu a ƙarƙashin sawunka ka kuma tura dukan kurakuranmu zuwa cikin zurfafan teku.
He will return and have mercy upon us; he will sink our iniquities, and they shall be cast into the depth of the sea, [even] all our sins.
20 Za ka yi wa Yaƙub aminci, ka kuma nuna jinƙai ga Ibrahim, kamar yadda ka yi alkawari da rantsuwa ga kakanninmu tun a kwanankin dā.
He shall give blessings truly to Jacob, and mercy to Abraam, as thou swarest to our fathers, according to the former days.