< Mika 6 >
1 Ku saurari abin da Ubangiji ya ce, “Tashi ku gabatar da ƙararku a gaban duwatsu; bari tuddai su ji abin da kuke so ku faɗa.
RAB'bin söylediğine kulak verin: Kalkın, davanızı dağların önünde dile getirin. Tepeler duysun sesinizi.
2 “Ku saurara, ya ku duwatsu game da tuhumar da Ubangiji yake muku, ku ji, ku daɗaɗɗun tushin duniya. Gama Ubangiji yana da ƙara a kan mutanensa; yana tuhumar Isra’ila.
Ey dağlar ve yeryüzünün sarsılmaz temelleri, RAB'bin suçlamasını dinleyin. Çünkü RAB halkından davacı, İsrail'den şikâyetçi.
3 “Ya ku mutanena, me na yi muku? Ta yaya na nawaita muku? Ku amsa mini.
“Ey halkım, sana ne yaptım?” diyor RAB, “Sana nasıl yük oldum, yanıtla.
4 Na fito da ku daga ƙasar Masar na kuma’yantar da ku daga ƙasar bauta. Na aika da Musa yă jagorance ku, haka ma Haruna da Miriyam.
Seni Mısır'dan ben çıkardım, Ben kurtardım seni kölelik diyarından. Sana öncülük etsinler diye Musa'yı, Harun'u, Miryam'ı ben gönderdim.
5 Ya ku mutanena, ku tuna abin da Balak sarkin Mowab ya ƙulla da kuma amsar da Bala’am ɗan Beyor ya bayar. Ku tuna da tafiyarku daga Shittim zuwa Gilgal, don ku san ayyukan adalcin Ubangiji.”
Ey halkım, Moav Kralı Balak'ın neler öğütlediğini, Beor oğlu Balam'ın onu nasıl yanıtladığını anımsa. Şittim'den Gilgal'a dek olup biteni an. Sizleri nasıl kurtardığımı o zaman anlayacaksın.”
6 Da me zan zo a gaban Ubangiji in rusuna a gaban Maɗaukaki Allah? Shin, zan zo ne a gabansa da hadaya ta ƙonawa, da ɗan maraƙi bana ɗaya?
RAB'bin önüne ne ile çıkayım, Yüce Tanrı'ya nasıl tapınayım? O'nun önüne yakmalık sunuyla mı, Bir yaşında danayla mı çıkayım?
7 Ubangiji zai ji daɗin hadayar raguna dubbai da kuma rafuffukan mai dubbai goma? Zan ba da ɗan farina ne don laifina, ko’ya’yan jikina domin zunubin raina?
Binlerce koç sunsam, Zeytinyağından on binlerce dere akıtsam, RAB hoşnut kalır mı? Suçuma karşılık ilk oğlumu, İşlediğim günah için bedenimin ürününü versem olur mu?
8 Ya nuna maka, ya mutum, abin da yake mai kyau. Me Ubangiji yake bukata daga gare ka kuwa shi ne ka yi gaskiya ka so aikata jinƙai ka kuma yi tafiya da tawali’u a gaban Allah.
Ey insanlar, RAB iyi olanı size bildirdi; Adil davranmanızdan, sadakati sevmenizden Ve alçakgönüllülükle yolunda yürümenizden başka Tanrınız RAB sizden ne istedi?
9 Ku saurara! Ubangiji yana kira ga birni, a ji tsoron sunana kuwa hikima ce, “Ku kasa kunne ga sandan nan da kuma wannan wanda ya naɗa.
Dinleyin! RAB kente sesleniyor. O'nun adından korkmak bilgeliktir. Diyor ki, “Ey halk ve kent meclisi, dinleyin.
10 Har yanzu zan manta, ya muguwar gida da dukiyarki da kika samu a muguwar hanya zan kuma manta da bugaggen mudun awo wanda ake zargi?
Kötü adamların evleri Haksızca kazanılmış servetlerle dolu, Bilmiyor muyum sanıyorsunuz? Eksik ölçek lanetlidir.
11 Zan kuɓutar da mutumin da yake da ma’auni na rashin gaskiya, da kuma buhun ma’aunan ƙarya?
Hileli terazi kullanan, Torbasında eksik ağırlıklar olan adamı nasıl aklayayım?
12 Attajiranta masu fitina ne; mutanenta kuma maƙaryata ne harsunansu kuwa suna yaudara.
Kentin zenginleri zorba, Halkı da yalancıdır. Dillerinden aldatıcı sözler dökülür.
13 Saboda haka, zan hallaka ku in lalace ku saboda zunubanku.
Günahlarınızdan ötürü yıkımınızı, Mahvınızı hazırladım bile.
14 Za ku ci amma ba za ku ƙoshi ba, cikinku zai zama babu kome Za ku tattara amma ba za ku yi ajiyar kome ba, gama abin da kuka yi ajiya zan ba wa takobi.
Yiyecek, ama doymayacaksınız. Aç kalacak karnınız, Biriktireceksiniz, ama saklayamayacaksınız. Koruyabildiğinizi kılıçla yok edeceğim.
15 Za ku yi shuki amma ba za ku girba ba; za ku matse zaitun amma ba za ku yi amfani da mai wa kanku ba, za ku tattaka’ya’yan inabi amma ba za ku sha ruwan inabin ba.
Ekecek, ama biçemeyeceksiniz. Zeytin ezecek, ama yağını sürünemeyeceksiniz. Üzümü sıkacak, ama şarabını içemeyeceksiniz.
16 Kuna kiyaye ƙa’idodin Omri da dukan ayyukan gidan Ahab kun kuma bi al’adunsu. Saboda haka, zan maishe ku kufai in mai da ku abin dariya a cikin mutane, za ku sha reni a wurin al’ummai.”
Kral Omri'nin buyruklarına, Ahav soyunun kötü adetlerine uyduğunuz, Onların törelerini izlediğiniz için sizi utanca boğacağım, yıkıma uğratacağım. Halkım olarak aşağılanmaya dayanmak zorunda kalacaksınız.”