< Mika 6 >

1 Ku saurari abin da Ubangiji ya ce, “Tashi ku gabatar da ƙararku a gaban duwatsu; bari tuddai su ji abin da kuke so ku faɗa.
Hear ye what Jehovah saith! Arise, contend thou before the mountains, And let the hills hear thy voice!
2 “Ku saurara, ya ku duwatsu game da tuhumar da Ubangiji yake muku, ku ji, ku daɗaɗɗun tushin duniya. Gama Ubangiji yana da ƙara a kan mutanensa; yana tuhumar Isra’ila.
Hear, O ye mountains, the controversy of Jehovah! Hear, ye strong foundations of the earth! For Jehovah hath a controversy with his people; He contendeth with Israel.
3 “Ya ku mutanena, me na yi muku? Ta yaya na nawaita muku? Ku amsa mini.
“O my people, what have I done to thee, And wherein have I offended thee? Testify against me!
4 Na fito da ku daga ƙasar Masar na kuma’yantar da ku daga ƙasar bauta. Na aika da Musa yă jagorance ku, haka ma Haruna da Miriyam.
I brought thee up from the land of Egypt, And from the house of bondage I redeemed thee; I sent Moses, Aaron, and Miriam, to go before thee.
5 Ya ku mutanena, ku tuna abin da Balak sarkin Mowab ya ƙulla da kuma amsar da Bala’am ɗan Beyor ya bayar. Ku tuna da tafiyarku daga Shittim zuwa Gilgal, don ku san ayyukan adalcin Ubangiji.”
O my people, remember what Balak the king of Moab devised. And what Balaam, the son of Beor, answered him, What happened from Shittim to Gilgal, That ye may know the mercies of Jehovah.”
6 Da me zan zo a gaban Ubangiji in rusuna a gaban Maɗaukaki Allah? Shin, zan zo ne a gabansa da hadaya ta ƙonawa, da ɗan maraƙi bana ɗaya?
Wherewith shall I come before Jehovah, And bow myself before the most high God? Shall I come before him with burnt-offerings, With calves of a year old?
7 Ubangiji zai ji daɗin hadayar raguna dubbai da kuma rafuffukan mai dubbai goma? Zan ba da ɗan farina ne don laifina, ko’ya’yan jikina domin zunubin raina?
Will Jehovah be pleased with thousands of rams, Or with ten thousands of rivers of oil? Shall I give my first-born for the sin of my soul, The fruit of my body for my transgression?
8 Ya nuna maka, ya mutum, abin da yake mai kyau. Me Ubangiji yake bukata daga gare ka kuwa shi ne ka yi gaskiya ka so aikata jinƙai ka kuma yi tafiya da tawali’u a gaban Allah.
He hath showed thee, O man, what is good; What doth Jehovah require of thee, But to do justly, and to love mercy, And to walk humbly before thy God?
9 Ku saurara! Ubangiji yana kira ga birni, a ji tsoron sunana kuwa hikima ce, “Ku kasa kunne ga sandan nan da kuma wannan wanda ya naɗa.
The voice of Jehovah crieth to the city, And the man of wisdom will discern thee; Hear ye the rod, and who hath threatened it!
10 Har yanzu zan manta, ya muguwar gida da dukiyarki da kika samu a muguwar hanya zan kuma manta da bugaggen mudun awo wanda ake zargi?
Are there not yet in the houses of the unrighteous the treasures of iniquity, And the scanty measure, which is abominable?
11 Zan kuɓutar da mutumin da yake da ma’auni na rashin gaskiya, da kuma buhun ma’aunan ƙarya?
Shall I count her pure with the wicked balances, And with the bag of deceitful weights?
12 Attajiranta masu fitina ne; mutanenta kuma maƙaryata ne harsunansu kuwa suna yaudara.
For her rich men are full of violence, And her inhabitants speak lies, And their tongue is deceitful in their mouth.
13 Saboda haka, zan hallaka ku in lalace ku saboda zunubanku.
Therefore will I sorely smite thee, And make thee desolate on account of thy sins.
14 Za ku ci amma ba za ku ƙoshi ba, cikinku zai zama babu kome Za ku tattara amma ba za ku yi ajiyar kome ba, gama abin da kuka yi ajiya zan ba wa takobi.
Thou shalt eat and not be satisfied, And hunger shall be within thee. Thou shalt remove, but shalt not save, And what thou savest will I give up to the sword.
15 Za ku yi shuki amma ba za ku girba ba; za ku matse zaitun amma ba za ku yi amfani da mai wa kanku ba, za ku tattaka’ya’yan inabi amma ba za ku sha ruwan inabin ba.
Thou shalt sow, but shalt not reap; Thou shalt tread the olives, but shalt not anoint thee with oil, And the grapes, but shalt not drink the wine.
16 Kuna kiyaye ƙa’idodin Omri da dukan ayyukan gidan Ahab kun kuma bi al’adunsu. Saboda haka, zan maishe ku kufai in mai da ku abin dariya a cikin mutane, za ku sha reni a wurin al’ummai.”
For ye keep the statutes of Omri, And all the works of the house of Ahab, And walk in their devices; Therefore will I make thee a desolation, And thine inhabitants a derision; And ye shall bear the reproach of my people.

< Mika 6 >