< Mika 6 >

1 Ku saurari abin da Ubangiji ya ce, “Tashi ku gabatar da ƙararku a gaban duwatsu; bari tuddai su ji abin da kuke so ku faɗa.
Hører dog, hvad Herren siger: Gør dig rede, tag Trætten op over for Bjergene, og lad Højene høre din Røst!
2 “Ku saurara, ya ku duwatsu game da tuhumar da Ubangiji yake muku, ku ji, ku daɗaɗɗun tushin duniya. Gama Ubangiji yana da ƙara a kan mutanensa; yana tuhumar Isra’ila.
Hører, I Bjerge! Herrens Trætte, og I uforanderlige, I Jordens Grundpiller! thi Herren har Trætte med sit Folk, og med Israel gaar han i Rette.
3 “Ya ku mutanena, me na yi muku? Ta yaya na nawaita muku? Ku amsa mini.
Mit Folk! hvad har jeg gjort dig, og hvormed har jeg voldet dig Møje? svar mig!
4 Na fito da ku daga ƙasar Masar na kuma’yantar da ku daga ƙasar bauta. Na aika da Musa yă jagorance ku, haka ma Haruna da Miriyam.
Thi jeg førte dig op fra Ægyptens Land, og fra Trælles Hus udløste jeg dig, og jeg sendte for dit Ansigt Mose, Aron og Maria.
5 Ya ku mutanena, ku tuna abin da Balak sarkin Mowab ya ƙulla da kuma amsar da Bala’am ɗan Beyor ya bayar. Ku tuna da tafiyarku daga Shittim zuwa Gilgal, don ku san ayyukan adalcin Ubangiji.”
Mit Folk! kom dog i Hu, hvad Raad Balak, Kongen af Moab, havde oplagt, og hvad Svar Bileam, Beors Søn, gav ham, og hvad der skete fra Sittim indtil Gilgal, for at du maa kende Herrens retfærdige Gerninger.
6 Da me zan zo a gaban Ubangiji in rusuna a gaban Maɗaukaki Allah? Shin, zan zo ne a gabansa da hadaya ta ƙonawa, da ɗan maraƙi bana ɗaya?
Hvormed skal jeg komme Herren i Møde og bøje mig for Højhedens Gud? mon jeg skal komme ham i Møde med Brændofre med aarsgamle Kalve?
7 Ubangiji zai ji daɗin hadayar raguna dubbai da kuma rafuffukan mai dubbai goma? Zan ba da ɗan farina ne don laifina, ko’ya’yan jikina domin zunubin raina?
Mon Herren vil have Behag i Tusinder af Vædre, i ti Tusinder af Oliebække? mon jeg skal give min førstefødte for min Overtrædelse, min Livsfrugt som Syndoffer for min Sjæl?
8 Ya nuna maka, ya mutum, abin da yake mai kyau. Me Ubangiji yake bukata daga gare ka kuwa shi ne ka yi gaskiya ka so aikata jinƙai ka kuma yi tafiya da tawali’u a gaban Allah.
Han har kundgjort dig, o Menneske! hvad godt er, og hvad Herren kræver af dig: Kun det at gøre Ret og at elske Miskundhed og at vandre ydmygelig med din Gud.
9 Ku saurara! Ubangiji yana kira ga birni, a ji tsoron sunana kuwa hikima ce, “Ku kasa kunne ga sandan nan da kuma wannan wanda ya naɗa.
Herrens Røst raaber til Staden — og dit Navn ser efter Visdom —; hører Riset! og hvo har beskikket det?
10 Har yanzu zan manta, ya muguwar gida da dukiyarki da kika samu a muguwar hanya zan kuma manta da bugaggen mudun awo wanda ake zargi?
Mon der i den ugudeliges Hus endnu er ugudeliges Skatte og en knap Efa, over hvilken der hviler Forbandelse?
11 Zan kuɓutar da mutumin da yake da ma’auni na rashin gaskiya, da kuma buhun ma’aunan ƙarya?
Mon man kan være ren med Ugudeligheds Vægtskaale, og med en Pose, hvori der er Falskheds Vægtlodder?
12 Attajiranta masu fitina ne; mutanenta kuma maƙaryata ne harsunansu kuwa suna yaudara.
Thi Rigmændene der ere fulde af Uretfærdighed, og Indbyggerne der tale Løgn, og deres Tunge er Falskhed i deres Mund!
13 Saboda haka, zan hallaka ku in lalace ku saboda zunubanku.
Saa vil da ogsaa jeg slaa dig smerteligt, idet jeg ødelægger dig for dine Synders Skyld.
14 Za ku ci amma ba za ku ƙoshi ba, cikinku zai zama babu kome Za ku tattara amma ba za ku yi ajiyar kome ba, gama abin da kuka yi ajiya zan ba wa takobi.
Du skal æde og ikke mættes, og din Hunger skal blive i dit Indre; og bringer du noget til Side, skal du ikke frelse det, og hvad du frelser, vil jeg overgive til Sværdet.
15 Za ku yi shuki amma ba za ku girba ba; za ku matse zaitun amma ba za ku yi amfani da mai wa kanku ba, za ku tattaka’ya’yan inabi amma ba za ku sha ruwan inabin ba.
Du skal saa og ikke høste; du skal presse Oliven, men ikke salve dig med Olie, og Most, men ikke drikke Vin.
16 Kuna kiyaye ƙa’idodin Omri da dukan ayyukan gidan Ahab kun kuma bi al’adunsu. Saboda haka, zan maishe ku kufai in mai da ku abin dariya a cikin mutane, za ku sha reni a wurin al’ummai.”
Og man holder omhyggeligt ved Omris Skikke og al Akabs Hus's Gerning, og I vandre i deres Raad, paa det jeg skal gøre dig til en Forfærdelse og Indbyggerne der til en Spot, og mit Folks Forsmædelse skulle I bære.

< Mika 6 >