< Mika 5 >
1 Ki tattara sojojinki, ya ke birnin mayaƙa, gama an kewaye mu da yaƙi. Za su bugi kumatun mai mulkin Isra’ila da sandar ƙarfe.
Maintenant, fille de troupes, rassemble tes troupes! On a mis le siège contre nous, on frappe de la verge sur la joue le juge d’Israël.
2 “Amma ke, Betlehem ta Efrata, ko da yake ke ƙarama ce daga cikin zuriyarki a Yahuda, daga cikinki wani zai zo domina wanda zai yi mulkin Isra’ila, wanda asalinsa tun fil azal ne.”
Et toi, Bethléem Ephrata, petite pour être entre les milliers de Juda, de toi sortira pour moi celui qui doit être dominateur en Israël, et ses origines dateront des temps anciens, des jours de l’éternité.
3 Saboda haka za a yashe Isra’ila har sai wadda take naƙuda ta haihu sauran’yan’uwansa kuma sun dawo su haɗu da Isra’ilawa.
C’est pourquoi il les livrera, jusqu’au temps où celle qui doit enfanter aura enfanté; et le reste de ses frères reviendra aux enfants d’Israël.
4 Zai tsaya yă yi kiwon garkensa da ƙarfin Ubangiji, cikin girman sunan Ubangiji Allahnsa. Za su kuma zauna lafiya, gama girmansa za tă kai har ƙarshen duniya.
Il se tiendra ferme, et il paîtra ses brebis, dans la force de Yahweh, dans la majesté du nom de Yahweh, son Dieu; et on demeurera en sécurité, car maintenant il sera grand, jusqu’aux extrémités de la terre.
5 Zai kuma zama salamarsu. Sa’ad da Assuriyawa suka kawo wa ƙasarmu hari suka tattake kagarunmu, za mu tā da makiyaya bakwai, har ma shugabannin mutane takwas su yi gāba da su.
C’est lui qui sera la paix. Quand l’Assyrien viendra dans notre pays, et que son pied foulera nos palais, nous ferons lever contre lui sept pasteurs, et huit princes du peuple.
6 Za su yi mulkin ƙasar Assuriya da takobi, ƙasar Nimrod kuma da zaran takobi. Zai cece mu daga hannun Assuriyawa sa’ad da suka kawo wa ƙasarmu hari suka kuma tattake zuwa cikin iyakokinmu.
Ils paîtront le pays d’Assur avec l’épée, et le pays de Nemrod dans ses portes; Il nous délivrera de l’Assyrien, lorsqu’il viendra dans notre pays, et que son pied foulera notre territoire.
7 Raguwar Yaƙub za tă kasance a tsakiyar mutane masu yawa kamar raɓa daga Ubangiji, kamar yayyafi a kan ciyawa, wanda ba ya jiran mutum ko kuma yă dakata wa ɗan adam.
Et le reste de Jacob sera, au milieu de peuples nombreux, comme une rosée venant de Yahweh, comme des gouttes de pluie sur le gazon, lequel n’attend personne, et n’espère pas dans les enfants des hommes.
8 Raguwar Yaƙub za tă kasance tare da al’ummai, a cikin mutane masu yawa, kamar zaki a cikin sauran namun jeji, kamar ɗan zaki cikin garken tumaki, wanda yake tattaka yă kuma yi kaca-kaca da su sa’ad da yake ratsa a cikinsu, ba kuwa wanda zai cece su.
Et le reste de Jacob sera aussi parmi les nations, au milieu de peuples nombreux, comme un lion parmi les bêtes de la forêt, comme un jeune lion parmi les troupeaux de brebis; lorsqu’il passe, foule et déchire, personne ne délivre.
9 Za a ɗaga hannunka cikin nasara a kan abokan gābanka, za a hallaka maƙiyanka duka.
Que votre main se lève contre vos adversaires, et que vos ennemis soient exterminés!
10 “A wannan rana,” in ji Ubangiji “Zan hallaka dawakanku daga cikinku, in kuma rurrushe kekunan yaƙinku.
En ce jour-là, — oracle de Yahweh, j’exterminerai tes chevaux du milieu de toi, et je détruirai tes chars.
11 Zan hallaka biranen ƙasarku in yi rugu-rugu da dukan katangunku.
Je ruinerai les villes de ton pays, et je démolirai toutes tes forteresses.
12 Zan kawar da maitarku, ba za a ƙara yin sihiri ba.
Je retrancherai de ta main les sortilèges, et il n’y aura plus chez toi de devins.
13 Zan sassare dukan gumakan da kuka sassaƙa da keɓaɓɓun duwatsunku a cikinku, nan gaba ba za ku ƙara rusuna wa aikin hannuwanku ba.
J’exterminerai du milieu de toi tes idoles et tes stèles, et tu n’adoreras plus l’ouvrage de tes mains.
14 Zan tumɓuke daga gare ku ginshiƙan Asheranku in kuma rurrushe biranenku.
J’arracherai du milieu de toi tes aschéras, et je détruirai tes villes.
15 Zan yi ramuwa cikin fushi da hasala a kan al’umman da ba su yi mini biyayya ba.”
Et dans ma colère et dans ma fureur, je tirerai vengeance des peuples qui n’auront pas écouté.