< Mika 5 >
1 Ki tattara sojojinki, ya ke birnin mayaƙa, gama an kewaye mu da yaƙi. Za su bugi kumatun mai mulkin Isra’ila da sandar ƙarfe.
‘Now cut yourself in bitter grief, daughter besieged by soldiers. They have set a wall around you. They strike the ruler of Israel, in the face with a rod.
2 “Amma ke, Betlehem ta Efrata, ko da yake ke ƙarama ce daga cikin zuriyarki a Yahuda, daga cikinki wani zai zo domina wanda zai yi mulkin Isra’ila, wanda asalinsa tun fil azal ne.”
‘Bethlehem in Ephrathah, small among the tribes of Judah, from you will come a king who will rule for me over Israel, whose family line goes back to the distant past.’
3 Saboda haka za a yashe Isra’ila har sai wadda take naƙuda ta haihu sauran’yan’uwansa kuma sun dawo su haɗu da Isra’ilawa.
So the Lord will only abandon Israel to its enemies until the woman in labour gives birth. Then the survivors will be reunited with their own people.
4 Zai tsaya yă yi kiwon garkensa da ƙarfin Ubangiji, cikin girman sunan Ubangiji Allahnsa. Za su kuma zauna lafiya, gama girmansa za tă kai har ƙarshen duniya.
And he will stand and shepherd by the strength of the Lord, In the exalted name of the Lord his God; And they will live in security, for now he will be great, even to the ends of the earth.
5 Zai kuma zama salamarsu. Sa’ad da Assuriyawa suka kawo wa ƙasarmu hari suka tattake kagarunmu, za mu tā da makiyaya bakwai, har ma shugabannin mutane takwas su yi gāba da su.
This will be our peace: when Assyria comes into our land and treads on our soil, we will raise up against him seven shepherds, eight leaders of men.
6 Za su yi mulkin ƙasar Assuriya da takobi, ƙasar Nimrod kuma da zaran takobi. Zai cece mu daga hannun Assuriyawa sa’ad da suka kawo wa ƙasarmu hari suka kuma tattake zuwa cikin iyakokinmu.
They will shepherd Assyria with a sword, and the land of Nimrod with bared blades. They will deliver us from Assyria, when they come into our land, and tread within our borders.
7 Raguwar Yaƙub za tă kasance a tsakiyar mutane masu yawa kamar raɓa daga Ubangiji, kamar yayyafi a kan ciyawa, wanda ba ya jiran mutum ko kuma yă dakata wa ɗan adam.
And the survivors of Jacob will be disbursed among the nations, in the midst of many peoples, like dew from the Lord, like showers on the grass, which don’t wait for people to come or linger for mortals.
8 Raguwar Yaƙub za tă kasance tare da al’ummai, a cikin mutane masu yawa, kamar zaki a cikin sauran namun jeji, kamar ɗan zaki cikin garken tumaki, wanda yake tattaka yă kuma yi kaca-kaca da su sa’ad da yake ratsa a cikinsu, ba kuwa wanda zai cece su.
And the survivors of Jacob will be disbursed among the nations, in the midst of many peoples, like a lion among the beasts of the forest, like a young lion among the sheep-folds, who, when he passes through, pounces. He savages his prey. There is no rescuer.
9 Za a ɗaga hannunka cikin nasara a kan abokan gābanka, za a hallaka maƙiyanka duka.
Let your hand triumph over your adversaries, let all your enemies be cut off.
10 “A wannan rana,” in ji Ubangiji “Zan hallaka dawakanku daga cikinku, in kuma rurrushe kekunan yaƙinku.
On that day, says the Lord: ‘I will slaughter your horses from your midst, and destroy your chariots.
11 Zan hallaka biranen ƙasarku in yi rugu-rugu da dukan katangunku.
I will devastate the cities in your land, and tear down your fortresses.
12 Zan kawar da maitarku, ba za a ƙara yin sihiri ba.
I will destroy your magic charms, and you will have no soothsayers.
13 Zan sassare dukan gumakan da kuka sassaƙa da keɓaɓɓun duwatsunku a cikinku, nan gaba ba za ku ƙara rusuna wa aikin hannuwanku ba.
I will cut down your idols and sacred pillars, and you will not worship any more the work of your hands.
14 Zan tumɓuke daga gare ku ginshiƙan Asheranku in kuma rurrushe biranenku.
I will uproot your sacred poles, and destroy your idols.
15 Zan yi ramuwa cikin fushi da hasala a kan al’umman da ba su yi mini biyayya ba.”
In my wrath and my anger I will seek vengeance on the nations that ignore me.’