< Mika 4 >

1 A kwanakin ƙarshe za a kafa dutsen haikalin Ubangiji yă zama babba a cikin duwatsu. Za a ɗaga shi sama da tuddai, mutane kuma za su riƙa ɗunguma zuwa gare shi.
И будет в последния дни явлена гора Господня, уготована над верхи гор, и вознесется выше холмов, и потщатся к ней людие,
2 Al’ummai da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, don mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Doka za tă fita daga Sihiyona, maganar Ubangiji kuma daga Urushalima.
и приидут языцы мнози и рекут: приидите, взыдем на гору Господню и в дом Бога Иаковля: и покажут нам путь Его, и пойдем по стезям Его: яко от Сиона изыдет закон, и слово Господне из Иерусалима,
3 Zai shari’anta tsakanin mutane yă kuma sulhunta tsakanin manyan al’ummai nesa da kuma kusa. Har su mai da takubansu su zama garemani, māsunsu kuma su zama wuƙaƙen askin itace. Al’umma ba za tă ɗauki takobi gāba da wata al’umma ba, ko a yi horarwa don yaƙi.
и разсудит среде людий многих и изобличит языки крепки даже до земли дальния: и раскуют мечы своя на рала и сулицы своя на серпы, и не ктому возмет язык на язык меча, и не научатся ксему воевати.
4 Kowa zai zauna a tushen kuringar inabinsa da tushen ɓaurensa, kuma ba wanda zai tsoratar da su, gama Ubangiji Maɗaukaki ne ya faɗa.
И почиет кийждо под лозою своею и кийждо под смоковницею своею, и не будет устрашающаго, зане уста Господа Вседержителя глаголаша сия.
5 Dukan al’ummai za su iya tafiya a cikin sunan allolinsu; mu dai za mu yi tafiya a cikin sunan Ubangiji Allahnmu har abada abadin.
Яко вси людие пойдут кийждо в путь свой, а мы пойдем во имя Господа Бога нашего в век и далечае.
6 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “zan tattara guragu; zan kuma tara masu zaman bauta, da waɗanda na sa suka damu.
В той день, глаголет Господь, соберу сокрушенную, и отриновенную прииму, и ихже отринух:
7 Zan mai da guragu su zama raguwa, waɗanda aka kora, su zama al’umma mai ƙarfi. Ubangiji zai yi mulkinsu a Dutsen Sihiyona daga wannan rana da kuma har abada.
и положу сокрушенную во останок и отриновенную в язык крепок, и воцарится Господь над ними в горе Сионе отныне и до века.
8 Game da ke, ya hasumiyar tsaron garke, Ya mafaka Diyar Sihiyona, za a maido miki da mulkinki na dā, sarauta kuma za tă zo wa Diyar Urushalima.”
И ты, столпе паствы мгляный, дщи Сионя, к тебе приидет и внидет власть первая, царство из Вавилона дщери Иерусалимли.
9 Don me yanzu kike kuka da ƙarfi, ba ki da sarki ne? Masu shawararki sun hallaka ne, da zafi ya cika ki kamar mace mai naƙuda?
И ныне вскую познала еси зло? Не бе ли тебе царя? Или совет твой погибе, яко обыдоша тя болезни, аки раждающия?
10 Ki yi birgima cikin zafin azaba, ya Diyar Sihiyona, kamar macen da take naƙuda, don yanzu dole ki bar birni ki kafa sansani a filin Allah. Za ki tafi Babilon; a can za a kuɓutar da ki. A can ne Ubangiji zai fanshe ki daga hannun maƙiyanki.
Болезнуй и мужайся и приближайся, дщи Сионя, яко раждающая: зане ныне изыдеши из града и вселишися на поли и дойдеши Вавилона: оттуду изимет тя и оттуду избавит тя Господь Бог твой от руки враг твоих.
11 Amma yanzu al’ummai da yawa suna gāba da ke. Suna cewa, “Bari a ƙazantar da ita, bari mu zuba wa Sihiyona ido.”
И ныне собрашася на тя языцы мнози глаголющии: порадуемся: и воззрят на Сион очи наши.
12 Amma ba su san tunanin Ubangiji ba; ba su fahimci shirinsa ba, shi da ya tattara su kamar dammuna a masussuka.
Сии же не разумеша помышления Господня и не домыслишася совета Его, яко собра их аки снопы гуменныя.
13 “Ki tashi ki yi sussuka, ya Diyar Sihiyona, gama zan ba ki ƙahonin ƙarfe; zan ba ki kofatan tagulla domin ki ragargaje al’ummai masu yawa.” Za ki ba Ubangiji dukan dukiyarsu da suka tara ta hanyar zamba, wadatarsu kuma ga Ubangiji dukan duniya.
Востани и измлати их, дщи Сионя, яко роги твоя положу железны и пазнокти твоя положу медяны, и истончиши люди многи, и возложиши Господеви множество их и крепость их Господеви всея земли.

< Mika 4 >