< Mika 4 >

1 A kwanakin ƙarshe za a kafa dutsen haikalin Ubangiji yă zama babba a cikin duwatsu. Za a ɗaga shi sama da tuddai, mutane kuma za su riƙa ɗunguma zuwa gare shi.
Mais il arrivera, aux derniers jours, que la montagne de la maison de l'Éternel sera établie au-dessus des montagnes, et elle s'élèvera par-dessus les collines, et les peuples y afflueront.
2 Al’ummai da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, don mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Doka za tă fita daga Sihiyona, maganar Ubangiji kuma daga Urushalima.
Et des nations nombreuses iront, et diront: Venez et montons à la montagne de l'Éternel, à la maison du Dieu de Jacob; il nous instruira de ses voies, et nous marcherons dans ses sentiers! Car la loi sortira de Sion, et la parole de l'Éternel, de Jérusalem.
3 Zai shari’anta tsakanin mutane yă kuma sulhunta tsakanin manyan al’ummai nesa da kuma kusa. Har su mai da takubansu su zama garemani, māsunsu kuma su zama wuƙaƙen askin itace. Al’umma ba za tă ɗauki takobi gāba da wata al’umma ba, ko a yi horarwa don yaƙi.
Il jugera entre des peuples nombreux, et sera l'arbitre de nations puissantes, jusqu'aux pays lointains; ils forgeront de leurs épées des hoyaux, et de leurs lances, des serpes; une nation ne lèvera plus l'épée contre l'autre, et on n'apprendra plus la guerre.
4 Kowa zai zauna a tushen kuringar inabinsa da tushen ɓaurensa, kuma ba wanda zai tsoratar da su, gama Ubangiji Maɗaukaki ne ya faɗa.
Mais chacun habitera sous sa vigne et sous son figuier, sans que personne les épouvante; car la bouche de l'Éternel des armées a parlé.
5 Dukan al’ummai za su iya tafiya a cikin sunan allolinsu; mu dai za mu yi tafiya a cikin sunan Ubangiji Allahnmu har abada abadin.
Quand tous les peuples marchent chacun au nom de son dieu, nous, nous marcherons au nom de l'Éternel notre Dieu, à toujours et à perpétuité!
6 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “zan tattara guragu; zan kuma tara masu zaman bauta, da waɗanda na sa suka damu.
En ce jour-là, dit l'Éternel, je rassemblerai les boiteux, je recueillerai ceux qui étaient chassés, ceux que j'avais maltraités;
7 Zan mai da guragu su zama raguwa, waɗanda aka kora, su zama al’umma mai ƙarfi. Ubangiji zai yi mulkinsu a Dutsen Sihiyona daga wannan rana da kuma har abada.
Et je ferai de ceux qui boitent un reste, et de ceux qui ont été éloignés une nation puissante; et l'Éternel régnera sur eux, à la montagne de Sion, dès lors et à toujours.
8 Game da ke, ya hasumiyar tsaron garke, Ya mafaka Diyar Sihiyona, za a maido miki da mulkinki na dā, sarauta kuma za tă zo wa Diyar Urushalima.”
Et toi, tour du troupeau, colline de la fille de Sion, jusqu'à toi viendra, à toi arrivera l'ancienne domination; la royauté sera à la fille de Jérusalem.
9 Don me yanzu kike kuka da ƙarfi, ba ki da sarki ne? Masu shawararki sun hallaka ne, da zafi ya cika ki kamar mace mai naƙuda?
Pourquoi maintenant pousses-tu des cris? N'y a-t-il pas de roi au milieu de toi, ou ton conseiller a-t-il péri, pour que la douleur t'ait saisie comme celle qui enfante?
10 Ki yi birgima cikin zafin azaba, ya Diyar Sihiyona, kamar macen da take naƙuda, don yanzu dole ki bar birni ki kafa sansani a filin Allah. Za ki tafi Babilon; a can za a kuɓutar da ki. A can ne Ubangiji zai fanshe ki daga hannun maƙiyanki.
Sois en travail et crie, fille de Sion, comme celle qui enfante! Car maintenant tu sortiras de la ville, et tu demeureras aux champs, et tu iras jusqu'à Babylone. Là tu seras délivrée; là, l'Éternel te rachètera de la main de tes ennemis.
11 Amma yanzu al’ummai da yawa suna gāba da ke. Suna cewa, “Bari a ƙazantar da ita, bari mu zuba wa Sihiyona ido.”
Et maintenant plusieurs nations se rassemblent contre toi, qui disent: “Qu'elle soit profanée, et que notre œil voie en Sion ce qu'il désire! “
12 Amma ba su san tunanin Ubangiji ba; ba su fahimci shirinsa ba, shi da ya tattara su kamar dammuna a masussuka.
Mais elles ne connaissent pas les pensées de l'Éternel, et elles ne comprennent pas son dessein; car il les a rassemblées comme des gerbes dans l'aire.
13 “Ki tashi ki yi sussuka, ya Diyar Sihiyona, gama zan ba ki ƙahonin ƙarfe; zan ba ki kofatan tagulla domin ki ragargaje al’ummai masu yawa.” Za ki ba Ubangiji dukan dukiyarsu da suka tara ta hanyar zamba, wadatarsu kuma ga Ubangiji dukan duniya.
Lève-toi et foule, fille de Sion! Car je te ferai une corne de fer et des ongles d'airain, et tu broieras des peuples nombreux, et je vouerai comme un interdit leur butin à l'Éternel, et leurs richesses au Seigneur de toute la terre.

< Mika 4 >