< Mika 4 >
1 A kwanakin ƙarshe za a kafa dutsen haikalin Ubangiji yă zama babba a cikin duwatsu. Za a ɗaga shi sama da tuddai, mutane kuma za su riƙa ɗunguma zuwa gare shi.
But it shall come to pass in the last days That the mountain of the house of Jehovah shall be established at the head of the mountains, And exalted above the hills; And the nations shall flow to it.
2 Al’ummai da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, don mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Doka za tă fita daga Sihiyona, maganar Ubangiji kuma daga Urushalima.
And many nations shall go, saying, “Come, let us go up to the mountain of Jehovah, To the house of the God of Jacob, That he may teach us his ways, And that we may walk in his paths!” For from Zion shall go forth a law, And the word of Jehovah from Jerusalem.
3 Zai shari’anta tsakanin mutane yă kuma sulhunta tsakanin manyan al’ummai nesa da kuma kusa. Har su mai da takubansu su zama garemani, māsunsu kuma su zama wuƙaƙen askin itace. Al’umma ba za tă ɗauki takobi gāba da wata al’umma ba, ko a yi horarwa don yaƙi.
He shall be a judge of many nations, And an umpire of many kingdoms afar off. They shall beat their swords into ploughshares, And their spears into pruning-hooks; Nation shall not lift up the sword against nation, Neither shall they learn war any more.
4 Kowa zai zauna a tushen kuringar inabinsa da tushen ɓaurensa, kuma ba wanda zai tsoratar da su, gama Ubangiji Maɗaukaki ne ya faɗa.
But they shall sit every one under his vine, And under his fig-tree, And none shall make them afraid; The mouth of Jehovah of hosts hath spoken it.
5 Dukan al’ummai za su iya tafiya a cikin sunan allolinsu; mu dai za mu yi tafiya a cikin sunan Ubangiji Allahnmu har abada abadin.
Though all the nations walk every one in the name of its God, Yet will we walk in the name of Jehovah our God for ever and ever.
6 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “zan tattara guragu; zan kuma tara masu zaman bauta, da waɗanda na sa suka damu.
In that day, saith Jehovah, I will gather the halting, And the far scattered I will assemble, And those whom I have afflicted.
7 Zan mai da guragu su zama raguwa, waɗanda aka kora, su zama al’umma mai ƙarfi. Ubangiji zai yi mulkinsu a Dutsen Sihiyona daga wannan rana da kuma har abada.
I will make the halting a remnant, And the far scattered a strong nation; And Jehovah shall reign over them in mount Zion, Henceforth, even forever.
8 Game da ke, ya hasumiyar tsaron garke, Ya mafaka Diyar Sihiyona, za a maido miki da mulkinki na dā, sarauta kuma za tă zo wa Diyar Urushalima.”
And thou, O tower of the flock, O hill of the daughter of Zion, to thee it shall come, To thee shall come the former dominion, Even the kingdom of the daughter of Jerusalem.
9 Don me yanzu kike kuka da ƙarfi, ba ki da sarki ne? Masu shawararki sun hallaka ne, da zafi ya cika ki kamar mace mai naƙuda?
And now why dost thou cry aloud? Is there no king within thee? Have thy counsellors perished, That pangs have taken hold of thee, as of a woman in travail?
10 Ki yi birgima cikin zafin azaba, ya Diyar Sihiyona, kamar macen da take naƙuda, don yanzu dole ki bar birni ki kafa sansani a filin Allah. Za ki tafi Babilon; a can za a kuɓutar da ki. A can ne Ubangiji zai fanshe ki daga hannun maƙiyanki.
Yea, writhe, and be in anguish, O daughter of Zion, like a woman in travail! For now shalt thou go forth from the city, and dwell in the field; Thou shalt go even to Babylon; Yet there shalt thou be delivered. Jehovah will redeem thee from the hand of thine enemies.
11 Amma yanzu al’ummai da yawa suna gāba da ke. Suna cewa, “Bari a ƙazantar da ita, bari mu zuba wa Sihiyona ido.”
Now many nations gather themselves against thee, Who say, Let her be polluted, And let our eyes gaze upon Zion!
12 Amma ba su san tunanin Ubangiji ba; ba su fahimci shirinsa ba, shi da ya tattara su kamar dammuna a masussuka.
But they know not the thoughts of Jehovah, And understand not his purposes; For he gathereth them as sheaves into the thrashing-floor.
13 “Ki tashi ki yi sussuka, ya Diyar Sihiyona, gama zan ba ki ƙahonin ƙarfe; zan ba ki kofatan tagulla domin ki ragargaje al’ummai masu yawa.” Za ki ba Ubangiji dukan dukiyarsu da suka tara ta hanyar zamba, wadatarsu kuma ga Ubangiji dukan duniya.
Arise and thrash, O daughter of Zion! For I will make thy horns iron, And thy hoofs brass; Thou shalt beat in pieces many nations, And thou shalt devote their spoils to Jehovah, Their substance to the Lord of the whole earth.