< Mika 3 >

1 Sa’an nan na ce, “Ku kasa kunne, ku shugabannin Yaƙub, ku masu mulkin gidan Isra’ila. Ya kamata ku san shari’a,
Eu disse, “Por favor, ouçam, seus chefes de Jacob, e governantes da casa de Israel: Não é para você conhecer a justiça?
2 ku da kuke ƙin abu mai kyau kuke ƙaunar mugunta, ku da kuke feɗe mutanena kuke tuge nama daga ƙasusuwansu;
Você que odeia o bem, e amar o mal; que lhes arrancam a pele, e sua carne de fora de seus ossos;
3 ku da kuke cin naman mutanena, ku feɗe fatar jikinsu kuke kakkarya ƙasusuwansu, kuke yayyanka su gunduwa-gunduwa kamar naman da za a toya, kamar naman da za a sa a dafa.”
que também comem a carne do meu povo, e descascar-lhes a pele de cima, e quebrar seus ossos, e cortá-los em pedaços, como para a panela, e como carne dentro do caldeirão.
4 Sa’an nan za su kira ga Ubangiji, amma ba zai amsa musu ba. A wannan lokaci zai ɓoye fuskarsa daga gare su saboda irin muguntar da suka yi.
Então eles irão chorar para Yahweh, mas ele não lhes responderá. Sim, ele esconderá seu rosto deles naquele momento, porque eles fizeram seus atos malignos”.
5 Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Game da annabawa masu ɓad da mutanena, in wani ya ciyar da su, sai su ce akwai ‘salama’ amma in bai ciyar da su ba, a shirye suke su kai masa hari.
Yahweh diz a respeito dos profetas que desviam meu povo para aqueles que alimentam seus dentes, eles proclamam, “Paz!” e quem não cuida de sua boca, eles preparam guerra contra ele:
6 Saboda haka dare yana zuwa a bisanku, ba tare da wahayi ba, kuma duhu, ba tare da duba ba. Rana za tă fāɗi wa annabawa, yini kuma zai zama musu duhu.
“Portanto, a noite acabou para você, sem visão, e é escuro para você, que você não divinize; e o sol se porá sobre os profetas, e o dia será negro sobre eles.
7 Masu gani za su ji kunya, masu duba kuma za su ji taƙaici. Dukansu za su rufe fuskokinsu gama ba amsa daga Allah.”
Os videntes ficarão desapontados, e os adivinhadores confundiram. Sim, todos eles devem cobrir os lábios, pois não há resposta de Deus”.
8 Amma game da ni, ina cike da iko ta wurin Ruhun Ubangiji da kuma adalci da ƙarfi, don a sanar da Yaƙub laifofinsa, ga Isra’ila kuma zunubinsa.
Mas quanto a mim, estou cheio de poder pelo Espírito de Yahweh, e de julgamento, e de poder, para declarar a Jacob sua desobediência, e para Israel seu pecado.
9 Ku ji wannan, ku shugabannin gidan Yaƙub, ku masu mulkin gidan Isra’ila, ku da kuke ƙyamar gaskiya, kuka karkatar duk abin da yake na gaskiya;
Por favor, ouçam isto, seus chefes da casa de Jacob, e governantes da casa de Israel, que abominam a justiça, e perverter toda a equidade,
10 kuka gina Sihiyona ta wurin zub da jini, Urushalima kuma ta wurin mugunta.
que constroem Zion com sangue, e Jerusalém com iniqüidade.
11 Hukunce-hukuncen shugabannin ƙasar na cin hanci ne, firistocinta kuma suna koyarwa don a biya su, annabawanta kuwa suna yin annabci don neman kuɗi. Duk da haka suna jingina a kan Ubangiji suna cewa, “Ba Ubangiji yana tare da mu ba? Ba bala’in da zai zo mana.”
Seus líderes julgam por subornos, e seus padres ensinam por um preço, e seus profetas contam fortunas por dinheiro; mas eles se apoiam em Yahweh, e dizem, “Yahweh não está entre nós? Nenhum desastre virá sobre nós”.
12 Don haka, saboda ku, za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuma ta zama tarin juji, tudun haikali kuwa zai zama kurmin ƙayayyuwa.
Portanto, Zion para seu bem será arado como um campo, e Jerusalém se tornará um amontoado de escombros, e a montanha do templo como os lugares altos de uma floresta.

< Mika 3 >