< Mika 3 >

1 Sa’an nan na ce, “Ku kasa kunne, ku shugabannin Yaƙub, ku masu mulkin gidan Isra’ila. Ya kamata ku san shari’a,
و گفتم: ای روسای یعقوب و‌ای داوران خاندان اسرائیل بشنوید! آیا بر شما نیست که انصاف را بدانید؟۱
2 ku da kuke ƙin abu mai kyau kuke ƙaunar mugunta, ku da kuke feɗe mutanena kuke tuge nama daga ƙasusuwansu;
آنانی که از نیکویی نفرت دارند و بر بدی مایل می‌باشند و پوست را از تن مردم و گوشت را از استخوانهای ایشان می‌کنند،۲
3 ku da kuke cin naman mutanena, ku feɗe fatar jikinsu kuke kakkarya ƙasusuwansu, kuke yayyanka su gunduwa-gunduwa kamar naman da za a toya, kamar naman da za a sa a dafa.”
و کسانی که گوشت قوم مرا می‌خورند و پوست ایشان را از تن ایشان می‌کنند و استخوانهای ایشان را خرد کرده، آنها را گویا در دیگ و مثل گوشت در پاتیل می‌ریزند.۳
4 Sa’an nan za su kira ga Ubangiji, amma ba zai amsa musu ba. A wannan lokaci zai ɓoye fuskarsa daga gare su saboda irin muguntar da suka yi.
آنگاه نزد خداونداستغاثه خواهند نمود و ایشان را اجابت نخواهدنمود بلکه روی خود را در آنزمان از ایشان خواهد پوشانید چونکه مرتکب اعمال زشت شده‌اند.۴
5 Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Game da annabawa masu ɓad da mutanena, in wani ya ciyar da su, sai su ce akwai ‘salama’ amma in bai ciyar da su ba, a shirye suke su kai masa hari.
خداوند درباره انبیایی که قوم مرا گمراه می‌کنند و به دندانهای خود می‌گزند و سلامتی راندا می‌کنند و اگر کسی چیزی به دهان ایشان نگذارد با او تدارک جنگ می‌بینند، چنین می‌گوید:۵
6 Saboda haka dare yana zuwa a bisanku, ba tare da wahayi ba, kuma duhu, ba tare da duba ba. Rana za tă fāɗi wa annabawa, yini kuma zai zama musu duhu.
از این جهت برای شما شب خواهدبود که رویا نبینید و ظلمت برای شما خواهد بود که فالگیری ننمایید. آفتاب بر انبیاء غروب خواهد کرد و روز بر ایشان تاریک خواهد شد.۶
7 Masu gani za su ji kunya, masu duba kuma za su ji taƙaici. Dukansu za su rufe fuskokinsu gama ba amsa daga Allah.”
وراییان خجل و فالگیران رسوا شده، جمیع ایشان لبهای خود را خواهند پوشانید چونکه از جانب خدا جواب نخواهد بود.۷
8 Amma game da ni, ina cike da iko ta wurin Ruhun Ubangiji da kuma adalci da ƙarfi, don a sanar da Yaƙub laifofinsa, ga Isra’ila kuma zunubinsa.
و لیکن من از قوت روح خداوند و از انصاف و توانایی مملو شده‌ام تایعقوب را از عصیان او و اسرائیل را از گناهش خبر دهم.۸
9 Ku ji wannan, ku shugabannin gidan Yaƙub, ku masu mulkin gidan Isra’ila, ku da kuke ƙyamar gaskiya, kuka karkatar duk abin da yake na gaskiya;
‌ای روسای خاندان یعقوب و‌ای داوران خاندان اسرائیل این را بشنوید! شما که ازانصاف نفرت دارید و تمامی راستی را منحرف می‌سازید.۹
10 kuka gina Sihiyona ta wurin zub da jini, Urushalima kuma ta wurin mugunta.
و صهیون را به خون و اورشلیم را به ظلم بنا می‌نمایید.۱۰
11 Hukunce-hukuncen shugabannin ƙasar na cin hanci ne, firistocinta kuma suna koyarwa don a biya su, annabawanta kuwa suna yin annabci don neman kuɗi. Duk da haka suna jingina a kan Ubangiji suna cewa, “Ba Ubangiji yana tare da mu ba? Ba bala’in da zai zo mana.”
روسای ایشان برای رشوه داوری می‌نمایند و کاهنان ایشان برای اجرت تعلیم می‌دهند و انبیای ایشان برای نقره فال می‌گیرند و بر خداوند توکل نموده، می‌گویند: آیاخداوند در میان ما نیست پس بلا به ما نخواهدرسید.۱۱
12 Don haka, saboda ku, za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuma ta zama tarin juji, tudun haikali kuwa zai zama kurmin ƙayayyuwa.
بنابراین صهیون به‌سبب شما مثل مزرعه شیار خواهد شد و اورشلیم به توده های سنگ و کوه خانه به بلندیهای جنگل مبدل خواهد گردید.۱۲

< Mika 3 >