< Mika 3 >
1 Sa’an nan na ce, “Ku kasa kunne, ku shugabannin Yaƙub, ku masu mulkin gidan Isra’ila. Ya kamata ku san shari’a,
I also said: Hear, O ye heads of Jacob, And ye leaders of the house of Israel! Is it not for you to administer justice?
2 ku da kuke ƙin abu mai kyau kuke ƙaunar mugunta, ku da kuke feɗe mutanena kuke tuge nama daga ƙasusuwansu;
But ye hate what is good, and love what is evil; Ye tear from men their skin, Yea, their flesh from their bones;
3 ku da kuke cin naman mutanena, ku feɗe fatar jikinsu kuke kakkarya ƙasusuwansu, kuke yayyanka su gunduwa-gunduwa kamar naman da za a toya, kamar naman da za a sa a dafa.”
Ye devour the flesh of my people, And strip them of their skin, And break their bones, And cut them in pieces, as for the pot, And as flesh for the caldron?
4 Sa’an nan za su kira ga Ubangiji, amma ba zai amsa musu ba. A wannan lokaci zai ɓoye fuskarsa daga gare su saboda irin muguntar da suka yi.
Then shall they cry to Jehovah, But he will not hear them; Yea, at that time will he hide his face from them, Because they have done iniquity.
5 Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Game da annabawa masu ɓad da mutanena, in wani ya ciyar da su, sai su ce akwai ‘salama’ amma in bai ciyar da su ba, a shirye suke su kai masa hari.
Thus saith Jehovah concerning the prophets, who deceive my people, Who, while they bite with their teeth, proclaim peace, But who, if one fill not their mouths, prepare war against him:
6 Saboda haka dare yana zuwa a bisanku, ba tare da wahayi ba, kuma duhu, ba tare da duba ba. Rana za tă fāɗi wa annabawa, yini kuma zai zama musu duhu.
Therefore shall night come upon you, so that ye shall have no vision, And darkness, so that ye shall not divine; The sun shall go down upon the prophets, And the day shall be dark to them.
7 Masu gani za su ji kunya, masu duba kuma za su ji taƙaici. Dukansu za su rufe fuskokinsu gama ba amsa daga Allah.”
Then shall the seers be ashamed, and the diviners confounded, So that all of them shall hide their faces, Because there is no answer from God.
8 Amma game da ni, ina cike da iko ta wurin Ruhun Ubangiji da kuma adalci da ƙarfi, don a sanar da Yaƙub laifofinsa, ga Isra’ila kuma zunubinsa.
But I am full of power, even of the spirit of Jehovah; Full of uprightness and courage, To declare to Jacob his transgression, And to Israel his sin.
9 Ku ji wannan, ku shugabannin gidan Yaƙub, ku masu mulkin gidan Isra’ila, ku da kuke ƙyamar gaskiya, kuka karkatar duk abin da yake na gaskiya;
O hear this, ye heads of the house of Jacob, And ye leaders of the house of Israel, Who abhor justice, And pervert all equity,
10 kuka gina Sihiyona ta wurin zub da jini, Urushalima kuma ta wurin mugunta.
Who build up Zion with blood, And Jerusalem with iniquity!
11 Hukunce-hukuncen shugabannin ƙasar na cin hanci ne, firistocinta kuma suna koyarwa don a biya su, annabawanta kuwa suna yin annabci don neman kuɗi. Duk da haka suna jingina a kan Ubangiji suna cewa, “Ba Ubangiji yana tare da mu ba? Ba bala’in da zai zo mana.”
Her heads judge for reward, And her priests teach for hire, And her prophets divine for money, And yet they lean upon Jehovah, saying, “Is not Jehovah in the midst of us? No evil can come upon us.”
12 Don haka, saboda ku, za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuma ta zama tarin juji, tudun haikali kuwa zai zama kurmin ƙayayyuwa.
Therefore because of you shall Zion be ploughed as a field, And Jerusalem become heaps of stones, And the mountain of the temple like the heights of a forest.