< Mika 3 >
1 Sa’an nan na ce, “Ku kasa kunne, ku shugabannin Yaƙub, ku masu mulkin gidan Isra’ila. Ya kamata ku san shari’a,
And I said, Hear, I pray you, ye heads of Jacob, and rulers of the house of Israel. Is it not for you to know justice?
2 ku da kuke ƙin abu mai kyau kuke ƙaunar mugunta, ku da kuke feɗe mutanena kuke tuge nama daga ƙasusuwansu;
Ye who hate the good, and love the evil, who pluck off their skin from off them, and their flesh from off their bones,
3 ku da kuke cin naman mutanena, ku feɗe fatar jikinsu kuke kakkarya ƙasusuwansu, kuke yayyanka su gunduwa-gunduwa kamar naman da za a toya, kamar naman da za a sa a dafa.”
who also eat the flesh of my people, and flay their skin from off them, and break their bones, and chop them in pieces, as for the pot, and as flesh within the caldron.
4 Sa’an nan za su kira ga Ubangiji, amma ba zai amsa musu ba. A wannan lokaci zai ɓoye fuskarsa daga gare su saboda irin muguntar da suka yi.
Then they shall cry to Jehovah, but he will not answer them. Yea, he will hide his face from them at that time, according as they have wrought evil in their doings.
5 Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Game da annabawa masu ɓad da mutanena, in wani ya ciyar da su, sai su ce akwai ‘salama’ amma in bai ciyar da su ba, a shirye suke su kai masa hari.
Thus says Jehovah concerning the prophets who make my people to err, who bite with their teeth, and cry, Peace. And he who does not put into their mouths, they even prepare war against him.
6 Saboda haka dare yana zuwa a bisanku, ba tare da wahayi ba, kuma duhu, ba tare da duba ba. Rana za tă fāɗi wa annabawa, yini kuma zai zama musu duhu.
Therefore it shall be night to you, that ye shall have no vision. And it shall be dark to you, that ye shall not divine. And the sun shall go down upon the prophets, and the day shall be black over them.
7 Masu gani za su ji kunya, masu duba kuma za su ji taƙaici. Dukansu za su rufe fuskokinsu gama ba amsa daga Allah.”
And the seers shall be put to shame, and the diviners confounded. Yea, they shall all cover their lips, for there is no answer from God.
8 Amma game da ni, ina cike da iko ta wurin Ruhun Ubangiji da kuma adalci da ƙarfi, don a sanar da Yaƙub laifofinsa, ga Isra’ila kuma zunubinsa.
But as for me, I am full of power by the Spirit of Jehovah, and of judgment, and of might, to declare to Jacob his transgression, and to Israel his sin.
9 Ku ji wannan, ku shugabannin gidan Yaƙub, ku masu mulkin gidan Isra’ila, ku da kuke ƙyamar gaskiya, kuka karkatar duk abin da yake na gaskiya;
Hear this, I pray you, ye heads of the house of Jacob, and rulers of the house of Israel, who abhor justice, and pervert all equity.
10 kuka gina Sihiyona ta wurin zub da jini, Urushalima kuma ta wurin mugunta.
They build up Zion with blood, and Jerusalem with iniquity.
11 Hukunce-hukuncen shugabannin ƙasar na cin hanci ne, firistocinta kuma suna koyarwa don a biya su, annabawanta kuwa suna yin annabci don neman kuɗi. Duk da haka suna jingina a kan Ubangiji suna cewa, “Ba Ubangiji yana tare da mu ba? Ba bala’in da zai zo mana.”
The heads of it judge for a bribe, and the priests of it teach for a wage, and the prophets of it divine for money. Yet they lean upon Jehovah, and say, Is not Jehovah in the midst of us? No evil shall come upon us.
12 Don haka, saboda ku, za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuma ta zama tarin juji, tudun haikali kuwa zai zama kurmin ƙayayyuwa.
Therefore for your sake Zion shall be plowed as a field, and Jerusalem shall become heaps, and the mountain of the house as the high places of a forest.