< Mika 2 >
1 Taku ta ƙare, ku da kuke shirya makirci, ku da kuke ƙulle-ƙullen mugunta a kan gadonku! Da gari ya waye sai ku fita ku aikata mugunta domin ikon aikatawa yana hannunku.
Тешко онима који смишљају безакоње и о злу се труде на постељама својим, и кад сване извршују, јер им је сила у руци.
2 Kukan yi ƙyashin gonaki ku kuma ƙwace su, ku yi ƙyashin gidaje ku kuma ƙwace. Kukan zalunci mutum, ku ƙwace masa gidansa, har ku ƙwace masa gādonsa.
Желе њиве, и отимају их; желе куће, и узимају; чине силу човеку и кући његовој, човеку и наследству његовом.
3 Saboda haka, Ubangiji ya ce, “Ina shirya wa waɗannan mutane bala’i, yadda ba za ku iya ceton kanku ba. Ba za ku ƙara tafiya kuna taƙama ba, gama zai zama lokacin bala’i ne.
Зато овако вели Господ: Ево, ја мислим зло том роду, из ког нећете извући вратове своје, нити ћете ходити поносито, јер ће бити зло време.
4 A wannan rana mutane za su yi muku ba’a za su yi muku gwalo da wannan waƙar makoki, ‘An lalatar da mu sarai; an rarraba mallakar mutanena. Ya ɗauke shi daga gare ni! Ya miƙa filayenmu ga maciyan amanarmu.’”
У оно време говориће се прича о вама, и нарицаће се жалосно говорећи: Пропадосмо; промени део народа мог. Како ми узе! Узевши њиве наше раздели.
5 Saboda haka ba za ku kasance da wani a taron jama’ar Ubangiji da zai raba ƙasar ta wurin jefa ƙuri’a ba.
Зато нећеш имати никога ко би ти повукао уже за жреб у збору Господњем.
6 “Kada ku yi annabci” in ji annabawansu. “Kada ku yi annabci game da waɗannan abubuwa; abin kunya ba zai same mu ba.”
Немојте пророковати, нека они пророкују; ако им не пророкују, неће одступити срамота.
7 Daidai ne a ce, ya gidan Yaƙub, “Ruhun Ubangiji yana fushi ne? Yana yin irin waɗannan abubuwa?” “Ashe, maganata ba tă amfane wanda ayyukansa suke daidai ba?
О ти, који се зовеш дом Јаковљев, је ли се умалио Дух Господњи? Јесу ли то дела Његова? Еда ли моје речи нису добре ономе који ходи право?
8 Ba da daɗewa ba mutanena sun tashi kamar magabci. Kun tuɓe riga mai tsada daga waɗanda suke wucewa ba tare da kun damu ba, sai ka ce mutanen da suke komowa daga yaƙi.
А народ се мој пре подиже као непријатељ; преко хаљине скидате плашт с оних који пролазе не бојећи се, који се враћају из боја.
9 Kun kori matan mutanena daga gidajensu masu daɗi. Kuka kawar da albarkata har abada daga wurin’ya’yansu.
Жене народа мог изгоните из милих кућа њихових, од деце њихове отимате славу моју навек.
10 Ku tafi, ku ba ni wuri! Gama wannan ba wurin hutunku ba ne, gama ya ƙazantu, ya zama kangon da ya wuce gyara.
Устаните и идите, јер ово није почивалиште; што се оскврни, погубиће вас погибљу великом.
11 In maƙaryaci da mazambaci ya zo ya ce, ‘Zan yi muku annabci ku sami wadataccen ruwan inabi da barasa,’ zai dai zama annabin da ya dace da wannan mutane ne!
Ако ко ходи за ветром и казује лажи говорећи: Пророковаћу ти за вино и за силовито пиће, тај ће бити пророк овом народу.
12 “Tabbatacce zan tattara ku duka, ya gidan Yaƙub; zan tattara ku raguwar Isra’ila. Zan kawo su wuri ɗaya kamar tumaki a cikin garke, kamar garke a wajen kiwonsa; wurin zai cika da mutane.
Доиста ћу те сабрати свог, Јакове, доиста ћу скупити остатак Израиљев; поставићу их заједно као овце восорске, као стадо усред тора њиховог, биће врева од људства.
13 Wanda ya fasa ƙofa ya buɗe, shi zai haura yă yi musu jagora, za su fashe bangon su fita. Sarkinsu zai wuce gabansu, Ubangiji kuma zai kasance a gaba.”
Пред њима ће ићи који разбија; они ће разбити и проћи кроз врата, и изаћи ће; и цар ће њихов ићи пред њима, и Господ ће бити пред њима.