< Mika 2 >
1 Taku ta ƙare, ku da kuke shirya makirci, ku da kuke ƙulle-ƙullen mugunta a kan gadonku! Da gari ya waye sai ku fita ku aikata mugunta domin ikon aikatawa yana hannunku.
Ve dem som tenker ut urett og emner på ondt mens de ligger på sitt leie! Så snart morgenen gryr, setter de det i verk, fordi det står i deres makt.
2 Kukan yi ƙyashin gonaki ku kuma ƙwace su, ku yi ƙyashin gidaje ku kuma ƙwace. Kukan zalunci mutum, ku ƙwace masa gidansa, har ku ƙwace masa gādonsa.
De attrår marker og røver dem, de attrår hus og tar dem, de gjør vold mot mannen og hans hus, mot bonden og hans arvelodd.
3 Saboda haka, Ubangiji ya ce, “Ina shirya wa waɗannan mutane bala’i, yadda ba za ku iya ceton kanku ba. Ba za ku ƙara tafiya kuna taƙama ba, gama zai zama lokacin bala’i ne.
Derfor sier Herren så: Se, jeg tenker ut ondt over denne slekt, ulykker som I ikke skal kunne ryste av eders hals, og I skal ikke kunne gå med høireist hode; for det blir en ond tid.
4 A wannan rana mutane za su yi muku ba’a za su yi muku gwalo da wannan waƙar makoki, ‘An lalatar da mu sarai; an rarraba mallakar mutanena. Ya ɗauke shi daga gare ni! Ya miƙa filayenmu ga maciyan amanarmu.’”
På den dag skal folk istemme en spottevise over eder og synge en klagesang. De skal si: Det er forbi, vi er rent ødelagt; mitt folks arvelodd skifter han ut til andre, se, hvorledes han tar den fra mig! Til frafalne deler han ut våre jorder.
5 Saboda haka ba za ku kasance da wani a taron jama’ar Ubangiji da zai raba ƙasar ta wurin jefa ƙuri’a ba.
Derfor skal du ingen ha som drar målesnor over nogen jordlodd i Herrens menighet.
6 “Kada ku yi annabci” in ji annabawansu. “Kada ku yi annabci game da waɗannan abubuwa; abin kunya ba zai same mu ba.”
Prek ikke! Så preker de. De må ikke preke om slikt, det blir ingen ende på skjellsord.
7 Daidai ne a ce, ya gidan Yaƙub, “Ruhun Ubangiji yana fushi ne? Yana yin irin waɗannan abubuwa?” “Ashe, maganata ba tă amfane wanda ayyukansa suke daidai ba?
Hvilket ord, du Jakobs hus! Mon Herren er snar til vrede? Eller er det således han pleier å gå frem? Er ikke mine ord gode mot den som vandrer ærlig?
8 Ba da daɗewa ba mutanena sun tashi kamar magabci. Kun tuɓe riga mai tsada daga waɗanda suke wucewa ba tare da kun damu ba, sai ka ce mutanen da suke komowa daga yaƙi.
Men for lenge siden har mitt folk reist sig som min fiende; I drar kappen av folk som går trygge forbi og er fredelig sinnede - så de bare har kjortelen igjen.
9 Kun kori matan mutanena daga gidajensu masu daɗi. Kuka kawar da albarkata har abada daga wurin’ya’yansu.
Mitt folks kvinner driver I ut av de hjem som var deres lyst; fra deres små barn tar I for alltid bort den pryd jeg har gitt dem.
10 Ku tafi, ku ba ni wuri! Gama wannan ba wurin hutunku ba ne, gama ya ƙazantu, ya zama kangon da ya wuce gyara.
Stå op og dra bort! For her er ikke eders hvilested, for eders urenhets skyld, som volder fordervelse, svær fordervelse.
11 In maƙaryaci da mazambaci ya zo ya ce, ‘Zan yi muku annabci ku sami wadataccen ruwan inabi da barasa,’ zai dai zama annabin da ya dace da wannan mutane ne!
Om nogen kom med munnsvær og svik og løi og sa: Jeg vil preke for dig om vin og om sterk drikk - han skulde være en predikant for dette folk.
12 “Tabbatacce zan tattara ku duka, ya gidan Yaƙub; zan tattara ku raguwar Isra’ila. Zan kawo su wuri ɗaya kamar tumaki a cikin garke, kamar garke a wajen kiwonsa; wurin zai cika da mutane.
Jeg vil samle dig, Jakob, samle eder så mange som I er; sanke sammen vil jeg det som er igjen av Israel, jeg vil føre dem sammen som får i en kve, som en hjord til sitt beite, så det larmer av mennesker.
13 Wanda ya fasa ƙofa ya buɗe, shi zai haura yă yi musu jagora, za su fashe bangon su fita. Sarkinsu zai wuce gabansu, Ubangiji kuma zai kasance a gaba.”
Veibryteren går foran dem, de bryter igjennem og drar frem gjennem porten og går ut av den; deres konge drar frem foran dem, og Herren i spissen for dem.