< Mika 2 >

1 Taku ta ƙare, ku da kuke shirya makirci, ku da kuke ƙulle-ƙullen mugunta a kan gadonku! Da gari ya waye sai ku fita ku aikata mugunta domin ikon aikatawa yana hannunku.
Malheur à ceux qui pensent à faire outrage, qui forgent le mal sur leurs lits, et qui l'exécutent dès le point du jour, parce qu'ils ont le pouvoir en main.
2 Kukan yi ƙyashin gonaki ku kuma ƙwace su, ku yi ƙyashin gidaje ku kuma ƙwace. Kukan zalunci mutum, ku ƙwace masa gidansa, har ku ƙwace masa gādonsa.
S'ils convoitent des possessions, ils les ont aussitôt ravies, et [s'ils convoitent] des maisons, ils les ont aussitôt prises; ainsi ils oppriment l'homme et sa maison, l'homme, dis-je, et son héritage.
3 Saboda haka, Ubangiji ya ce, “Ina shirya wa waɗannan mutane bala’i, yadda ba za ku iya ceton kanku ba. Ba za ku ƙara tafiya kuna taƙama ba, gama zai zama lokacin bala’i ne.
C'est pourquoi ainsi a dit l'Eternel: Voici, je pense contre cette famille-ci un mal duquel vous ne pourrez point vous mettre à couvert, et vous ne marcherez point à tête levée; car ce temps [est] mauvais.
4 A wannan rana mutane za su yi muku ba’a za su yi muku gwalo da wannan waƙar makoki, ‘An lalatar da mu sarai; an rarraba mallakar mutanena. Ya ɗauke shi daga gare ni! Ya miƙa filayenmu ga maciyan amanarmu.’”
En ce temps-là on fera de vous un proverbe lugubre, et l'on gémira d'un gémissement lamentable, en disant: Nous sommes entièrement détruits, il a changé la portion de mon peuple; comment nous l'aurait-il ôtée? partage-t-il nos champs, pour nous les faire rendre?
5 Saboda haka ba za ku kasance da wani a taron jama’ar Ubangiji da zai raba ƙasar ta wurin jefa ƙuri’a ba.
C'est pourquoi il n'y aura personne pour toi qui jette le cordeau pour ton lot dans la congrégation de l'Eternel.
6 “Kada ku yi annabci” in ji annabawansu. “Kada ku yi annabci game da waɗannan abubuwa; abin kunya ba zai same mu ba.”
[On dit]: Ne prophétisez point, ils prophétiseront, [mais] ils ne prophétiseront point pour ceux-ci; l'ignominie ne tournera point en arrière.
7 Daidai ne a ce, ya gidan Yaƙub, “Ruhun Ubangiji yana fushi ne? Yana yin irin waɗannan abubuwa?” “Ashe, maganata ba tă amfane wanda ayyukansa suke daidai ba?
Or toi qui es appelée Maison de Jacob, l'Esprit de l'Eternel est-il amoindri? Sont-ce là ses actes? Mes paroles ne sont-elles pas bonnes pour celui qui marche droitement?
8 Ba da daɗewa ba mutanena sun tashi kamar magabci. Kun tuɓe riga mai tsada daga waɗanda suke wucewa ba tare da kun damu ba, sai ka ce mutanen da suke komowa daga yaƙi.
Mais celui qui était hier mon peuple, s'élève à la manière d'un ennemi, pour rencontrer un manteau; vous dépouillez le vêtement magnifique à ceux qui passent en assurance, étant de retour de la guerre.
9 Kun kori matan mutanena daga gidajensu masu daɗi. Kuka kawar da albarkata har abada daga wurin’ya’yansu.
Vous mettez les femmes de mon peuple hors des maisons où elles prenaient plaisir; vous ôtez pour jamais ma gloire de dessus leurs petits enfants.
10 Ku tafi, ku ba ni wuri! Gama wannan ba wurin hutunku ba ne, gama ya ƙazantu, ya zama kangon da ya wuce gyara.
Levez-vous, et marchez, car [ce pays] ne [vous est] plus [un lieu de] repos; parce qu'il est souillé, il [vous] détruira, même d'une prompte destruction.
11 In maƙaryaci da mazambaci ya zo ya ce, ‘Zan yi muku annabci ku sami wadataccen ruwan inabi da barasa,’ zai dai zama annabin da ya dace da wannan mutane ne!
S'il y a quelque homme qui marche selon le vent, et qui mente faussement, [en disant]; Je te prophétiserai du vin et de la cervoise; ce sera le Prophète de ce peuple.
12 “Tabbatacce zan tattara ku duka, ya gidan Yaƙub; zan tattara ku raguwar Isra’ila. Zan kawo su wuri ɗaya kamar tumaki a cikin garke, kamar garke a wajen kiwonsa; wurin zai cika da mutane.
[Mais] je t'assemblerai tout entier, ô Jacob! et je ramasserai entièrement le reste d'Israël, et le mettrai tout ensemble comme les brebis de Botsra, comme un troupeau au milieu de son étable; il y aura un grand bruit pour la foule des hommes.
13 Wanda ya fasa ƙofa ya buɗe, shi zai haura yă yi musu jagora, za su fashe bangon su fita. Sarkinsu zai wuce gabansu, Ubangiji kuma zai kasance a gaba.”
Le briseur montera devant eux, on brisera, et on passera outre, et eux sortiront par la porte; et leur Roi passera devant eux, et l'Eternel sera à leur tête.

< Mika 2 >