< Mika 2 >

1 Taku ta ƙare, ku da kuke shirya makirci, ku da kuke ƙulle-ƙullen mugunta a kan gadonku! Da gari ya waye sai ku fita ku aikata mugunta domin ikon aikatawa yana hannunku.
Woe to those who lie awake planning evil, who in the light of morning carry out their plan because they have the power to do it.
2 Kukan yi ƙyashin gonaki ku kuma ƙwace su, ku yi ƙyashin gidaje ku kuma ƙwace. Kukan zalunci mutum, ku ƙwace masa gidansa, har ku ƙwace masa gādonsa.
They covet fields and seize them, desire houses and take them, they crush householder and his household, people and their possessions.
3 Saboda haka, Ubangiji ya ce, “Ina shirya wa waɗannan mutane bala’i, yadda ba za ku iya ceton kanku ba. Ba za ku ƙara tafiya kuna taƙama ba, gama zai zama lokacin bala’i ne.
Therefore the Lord says: ‘I am planning disaster from which you cannot save your neck, nor walk proudly because it will be a terrible time.
4 A wannan rana mutane za su yi muku ba’a za su yi muku gwalo da wannan waƙar makoki, ‘An lalatar da mu sarai; an rarraba mallakar mutanena. Ya ɗauke shi daga gare ni! Ya miƙa filayenmu ga maciyan amanarmu.’”
On that day they will sing a taunt-song to you, this mocking lament: “My people’s estate is being measured for sale, our captors are dividing our fields. We are completely undone.”
5 Saboda haka ba za ku kasance da wani a taron jama’ar Ubangiji da zai raba ƙasar ta wurin jefa ƙuri’a ba.
There will be no one to measure out land for you from the Lord’s community.
6 “Kada ku yi annabci” in ji annabawansu. “Kada ku yi annabci game da waɗannan abubuwa; abin kunya ba zai same mu ba.”
‘“Don’t rant!” they urge, “Of such things one does not prophesy! Shame will not overtake us!
7 Daidai ne a ce, ya gidan Yaƙub, “Ruhun Ubangiji yana fushi ne? Yana yin irin waɗannan abubuwa?” “Ashe, maganata ba tă amfane wanda ayyukansa suke daidai ba?
Is the Lord impatient, or are such things his deeds? Are not his words favourable to the family of Jacob?” Aren’t my commands good for those who obey them?
8 Ba da daɗewa ba mutanena sun tashi kamar magabci. Kun tuɓe riga mai tsada daga waɗanda suke wucewa ba tare da kun damu ba, sai ka ce mutanen da suke komowa daga yaƙi.
But you, you stand up as a foe against those who are peaceful; you strip the robe from those who pass by quietly, averse to conflict.
9 Kun kori matan mutanena daga gidajensu masu daɗi. Kuka kawar da albarkata har abada daga wurin’ya’yansu.
Women of my people you drive out from their happy homes, from their young children you take away my glory forever.
10 Ku tafi, ku ba ni wuri! Gama wannan ba wurin hutunku ba ne, gama ya ƙazantu, ya zama kangon da ya wuce gyara.
Rise and begone, for this is no place to rest. Your uncleanness brings destruction, severe destruction.
11 In maƙaryaci da mazambaci ya zo ya ce, ‘Zan yi muku annabci ku sami wadataccen ruwan inabi da barasa,’ zai dai zama annabin da ya dace da wannan mutane ne!
If a person walking in wine and falsehood were to say, “I will prophesy to you of wine and strong drink,” then he would be the perfect prophet for this people!’
12 “Tabbatacce zan tattara ku duka, ya gidan Yaƙub; zan tattara ku raguwar Isra’ila. Zan kawo su wuri ɗaya kamar tumaki a cikin garke, kamar garke a wajen kiwonsa; wurin zai cika da mutane.
‘I will assuredly assemble all of Jacob, I will surely gather the survivors of Israel. I will herd them together as sheep in a fold, like a flock in the pasture, and the land will resound with the sounds of multitudes.
13 Wanda ya fasa ƙofa ya buɗe, shi zai haura yă yi musu jagora, za su fashe bangon su fita. Sarkinsu zai wuce gabansu, Ubangiji kuma zai kasance a gaba.”
‘The one who breaks out goes first. They have broken forth and passed by the gate and through it have they gone out. Their king leads before them, the Lord at their head.’

< Mika 2 >