< Mika 2 >
1 Taku ta ƙare, ku da kuke shirya makirci, ku da kuke ƙulle-ƙullen mugunta a kan gadonku! Da gari ya waye sai ku fita ku aikata mugunta domin ikon aikatawa yana hannunku.
Woe to you that devise that which is unprofitable, and work evil in your beds: in the morning light they execute it, because their hand is against God.
2 Kukan yi ƙyashin gonaki ku kuma ƙwace su, ku yi ƙyashin gidaje ku kuma ƙwace. Kukan zalunci mutum, ku ƙwace masa gidansa, har ku ƙwace masa gādonsa.
And they have coveted fields, and taken them by violence, and houses they have forcibly taken away: and oppressed a man and his house, a man and his inheritance.
3 Saboda haka, Ubangiji ya ce, “Ina shirya wa waɗannan mutane bala’i, yadda ba za ku iya ceton kanku ba. Ba za ku ƙara tafiya kuna taƙama ba, gama zai zama lokacin bala’i ne.
Therefore thus saith the Lord: Behold, I devise an evil against this family: from which you shall not withdraw your necks, and you shall not walk haughtily, for this is a very evil time.
4 A wannan rana mutane za su yi muku ba’a za su yi muku gwalo da wannan waƙar makoki, ‘An lalatar da mu sarai; an rarraba mallakar mutanena. Ya ɗauke shi daga gare ni! Ya miƙa filayenmu ga maciyan amanarmu.’”
In that day a parable shall be taken up upon you, and a song shall be sung with melody by them that say: We are laid waste and spoiled: the portion of my people is changed: how shall he depart from me, whereas he is returning that will divide our land?
5 Saboda haka ba za ku kasance da wani a taron jama’ar Ubangiji da zai raba ƙasar ta wurin jefa ƙuri’a ba.
Therefore thou shalt have none that shall cast the cord of a lot in the assembly of the Lord.
6 “Kada ku yi annabci” in ji annabawansu. “Kada ku yi annabci game da waɗannan abubuwa; abin kunya ba zai same mu ba.”
Speak ye not, saying: It shall not drop upon these, confusion shall not take them.
7 Daidai ne a ce, ya gidan Yaƙub, “Ruhun Ubangiji yana fushi ne? Yana yin irin waɗannan abubuwa?” “Ashe, maganata ba tă amfane wanda ayyukansa suke daidai ba?
The house of Jacob saith: Is the spirit of the Lord straitened, or are these his thoughts? Are not my words good to him that walketh uprightly?
8 Ba da daɗewa ba mutanena sun tashi kamar magabci. Kun tuɓe riga mai tsada daga waɗanda suke wucewa ba tare da kun damu ba, sai ka ce mutanen da suke komowa daga yaƙi.
But my people, on the contrary, are risen up as an enemy: you have taken away the cloak off from the coat: and them that passed harmless you have turned to war.
9 Kun kori matan mutanena daga gidajensu masu daɗi. Kuka kawar da albarkata har abada daga wurin’ya’yansu.
You have cast out the women of my people from their houses, in which they took delight: you have taken my praise for ever from their children.
10 Ku tafi, ku ba ni wuri! Gama wannan ba wurin hutunku ba ne, gama ya ƙazantu, ya zama kangon da ya wuce gyara.
Arise ye, and depart, for there is no rest here for you. For that uncleanness of the land, it shall be corrupted with a grievous corruption.
11 In maƙaryaci da mazambaci ya zo ya ce, ‘Zan yi muku annabci ku sami wadataccen ruwan inabi da barasa,’ zai dai zama annabin da ya dace da wannan mutane ne!
Would God I were not a man that hath the spirit, and that I rather spoke a lie: I will let drop to thee of wine, and of drunkenness: and it shall be this people upon whom it shall drop.
12 “Tabbatacce zan tattara ku duka, ya gidan Yaƙub; zan tattara ku raguwar Isra’ila. Zan kawo su wuri ɗaya kamar tumaki a cikin garke, kamar garke a wajen kiwonsa; wurin zai cika da mutane.
I will assemble and gather together all of thee, O Jacob: I will bring together the remnant of Israel, I will put them together as a flock in the fold, as the sheep in the midst of the sheepcotes, they shall make a tumult by reason of the multitude of men.
13 Wanda ya fasa ƙofa ya buɗe, shi zai haura yă yi musu jagora, za su fashe bangon su fita. Sarkinsu zai wuce gabansu, Ubangiji kuma zai kasance a gaba.”
For he shall go up that shall open the way before them: they shall divide, and pass through the gate, and shall come in by it: and their king shall pass before them, and the Lord at the head of them.