< Mika 1 >
1 Maganar Ubangiji ta zo wa Mika mutumin Moreshet a zamanin Yotam, da na Ahaz, da kuma na Hezekiya, sarakunan Yahuda, Mika ya ga wahayi a kan Samariya da kuma a kan Urushalima. Ga abin da ya ce.
Ty tsara’ Iehovà niheo amy Mikà nte-Moresete tañ’andro’ Iotame naho i Akhaze vaho Iekezkia mpanjaka’ Iehoda; i nioni’e ty amy Somerone naho Ierosalaimey.
2 Ku ji, ya ku mutane duka, ki saurara, ya ke duniya da dukan mazauna cikinki, bari Ubangiji Mai Iko Duka yă zama shaida a kanku, daga haikalinsa mai tsarki.
Kila mijanjiña ry ondatio; mañaoña ry tane, naho ze hene ama’e ao; fa hanesek’ anahareo t’Iehovà Talè, i Talè boak’añ’Anjomba’e Masiñe.
3 Duba! Ubangiji yana zuwa daga wurin zamansa; zai sauko yă taka maɗaukakan wuraren duniya.
Heheke te miavotse i toe’ey t’Iehovà, hizotso mb’etoa, handialia o haboa’ ty tane toio.
4 Duwatsu za su narke a ƙarƙashin ƙafafunsa, kamar kaki a gaban wuta, kwaruruka kuma za su ɓace, kamar ruwan da yake gangarowa daga tsauni.
Hitranak’ ambane’e eo o vohitseo, naho ho vaky o vavataneo, manahake ty takafotse añatrefa’ ty afo eo, naho rano nadoandoañe am-piroroñañe.
5 Duk wannan zai faru saboda laifin Yaƙub, da kuma zunuban gidan Isra’ila ne. Mene ne laifin Yaƙub? Shin, ba Samariya ba ce? Ina ne maɗaukakan wuraren Yahuda? Shin, ba Urushalima ba ce?
Fonga ty amo fiolà’ Iakobeo, naho o tahi’ i anjomba’ Israeleio; Ino i hakeo’ Iakobey? Tsy i Somerone hao? Aia o ankaboa’ Iehodao? Tsy e Ierosalaime hao?
6 “Saboda haka zan mai da Samariya tarin juji, wurin noman inabi. Zan zubar da duwatsunta a cikin kwari in kuma bar harsashin gininta a bayyane.
Aa le hanoeko fivotrim-porompotse an-tetek’ ao ty Somerone, ho tanem-bahe; naho haparatsiako am-bavatane ao o vato’eo, vaho haboako o mananta’eo.
7 Za a ragargaje dukan allolinta; za a ƙone dukan baye-bayenta na haikali da wuta; zan lalatar da dukan gumakanta. Tun da ta wurin karuwanci ne ta tattara su, ga karuwanci kuma za su koma.”
Ho demodemoheñe iaby o samposampo’eo, le ho forototoeñe añ’afo ao o nibanabanaeñe ama’eo; ho rotsaheko iaby o saren-drahare’eo, fa natonto’e an-tamben-karapilo, le hibalike ho tamben-tsimirirañe.
8 Saboda wannan zan yi baƙin ciki, in yi kuka; zan yi tafiya ba takalmi, zan tuɓe, in kuma yi tafiya tsirara. Zan yi kuka kamar dila, in yi baƙin ciki kamar mujiya.
Aa le hangoihoy naho hikoiakoiake iraho, hihalo naho hibongy te handeha; hanao fitrèn-drimo vaho fandalàm-boron-tsatrañe.
9 Gama raunin Samariya ba mai warkewa ba ne; ya bazu har Yahuda. Ya ma kai bakin ƙofar mutanena, har ma Urushalima da kanta.
Tsy lefe hahàñe o fere’eo, fa nandakake mb’e Iehoda ao; fa nahatakatse ty lalambei’ ondatikoo; Eka, pak’ e Ierosalaime ao.
10 Kada a faɗe shi a Gat; kada ma a yi kuka. A maimako haka, a yi birgima a cikin ƙura a Bet-Leyafra.
Ko taroñe’o e Gate añe, ko mirovetse; mivarimbariña an-davenok’ ao ty amy anjomba’ i Ofrày.
11 Ku wuce tsirara da kuma kunya, ku mazaunan Shafir. Bet-Ezel tana makoki domin babu wani daga Za’anan da ya fito don yă taimaka.
Mihelaña mb’eo ry mpimoneñe e Safire ao; ami’ty hameñaram-piboridaña’o; tsy lefe ty fivoratsaha’ o mpimone’ i Tsa’ananeo; mangololoike ty Bete’haetsele hasinta’e ama’o ty fijohaña’o.
12 Mazaunan Marot sun ƙosa su ga alheri, amma Ubangiji ya sauko da azaba, har zuwa ƙofar Urushalima.
Mifeak’ am-pitamàñe hasoa o mpimone’ i Maròteo fe nivotrak’ an-dalambei’ Ierosalaime eo boak’ am’ Iehovà ty hankàñe.
13 Ku da kuke zama a Lakish, ku ɗaura wa dawakai kekunan yaƙi. Gama ku kuka fara yin zunubi a Sihiyona, gama an sami laifofin Isra’ila a cikinku.
Feheo amo sareteo o soavalao, ry mpimone’ i Lakìse, ihe namototse ty hakeo’ i anak’ ampela’ i Tsioney, vaho nizoeñe ama’o o fiolà’ Israeleo.
14 Saboda haka za ku ba da kyautan bankwana ga Moreshet Gat. Garin Akzib zai zama abin yaudara ga sarakunan Isra’ila.
Aa le ho banabanae’o ravoravom-piavotañe ty Moresete-Gate; ho famañahiañe amo mpanjaka’ Israeleo o anjomba’ i Akzìbeo.
15 Ku mazaunan Maresha Ubangiji zai kawo wanda zai ci ku da yaƙi. Sarakunan Isra’ila za su gudu zuwa Adullam.
Mbore haseseko ama’o ty mpitavañe, ry mpimone’ i Maresà; himoak’ Adolame ao ty enge’ Israele.
16 Ku aske kanku ƙwal don makoki, ku yi wa kanku ƙwalƙwal kamar ungulu. Gama za a ja’ya’yan da kuke farin ciki a kai su bauta.
Mipeaha irehe, miharata ty amo anake mahafale azoo; indrao ty hasola’o hifanahak’ ami’ty koáke, ie hieng’azo mb’an-drohy mb’eo.