< Mika 1 >

1 Maganar Ubangiji ta zo wa Mika mutumin Moreshet a zamanin Yotam, da na Ahaz, da kuma na Hezekiya, sarakunan Yahuda, Mika ya ga wahayi a kan Samariya da kuma a kan Urushalima. Ga abin da ya ce.
The word of the Lord that came to Micah the Moreshethite, in the days of Jotham, Ahaz, and Hezekiah, kings of Judah, which he saw about Samaria and Jerusalem.
2 Ku ji, ya ku mutane duka, ki saurara, ya ke duniya da dukan mazauna cikinki, bari Ubangiji Mai Iko Duka yă zama shaida a kanku, daga haikalinsa mai tsarki.
All peoples, listen. And may the earth and its fullness pay attention. And may the Lord God be a witness to you, the Lord from his holy temple.
3 Duba! Ubangiji yana zuwa daga wurin zamansa; zai sauko yă taka maɗaukakan wuraren duniya.
For behold, the Lord will go forth from his place. And he will descend, and he will trample over the high places of the earth.
4 Duwatsu za su narke a ƙarƙashin ƙafafunsa, kamar kaki a gaban wuta, kwaruruka kuma za su ɓace, kamar ruwan da yake gangarowa daga tsauni.
And the mountains will be consumed under him, and the valleys will be torn apart, like wax before the face of fire, and like waters that rush swiftly downward.
5 Duk wannan zai faru saboda laifin Yaƙub, da kuma zunuban gidan Isra’ila ne. Mene ne laifin Yaƙub? Shin, ba Samariya ba ce? Ina ne maɗaukakan wuraren Yahuda? Shin, ba Urushalima ba ce?
All this is for the wickedness of Jacob and for the sins of the house of Israel. What is the wickedness of Jacob? Is it not Samaria? And what is the loftiness of Judah? Is it not Jerusalem?
6 “Saboda haka zan mai da Samariya tarin juji, wurin noman inabi. Zan zubar da duwatsunta a cikin kwari in kuma bar harsashin gininta a bayyane.
And I will place Samaria like a pile of stones in the field, when a vineyard is planted. And I will pull down its stones into the valley, and I will reveal her foundations.
7 Za a ragargaje dukan allolinta; za a ƙone dukan baye-bayenta na haikali da wuta; zan lalatar da dukan gumakanta. Tun da ta wurin karuwanci ne ta tattara su, ga karuwanci kuma za su koma.”
And all her graven images will be cut to pieces, and all her rewards will be burned with fire, and I will place all her idols in perdition. For they have been gathered together from the pay of a kept woman, and even to the pay of a kept woman, they will return.
8 Saboda wannan zan yi baƙin ciki, in yi kuka; zan yi tafiya ba takalmi, zan tuɓe, in kuma yi tafiya tsirara. Zan yi kuka kamar dila, in yi baƙin ciki kamar mujiya.
I will lament and wail about this. I will go out despoiled and naked. I will make a howl like the dragons, and a mourning like the ostriches.
9 Gama raunin Samariya ba mai warkewa ba ne; ya bazu har Yahuda. Ya ma kai bakin ƙofar mutanena, har ma Urushalima da kanta.
For her wound has been in despair. For it has come even to Judah. It has touched the gate of my people, even to Jerusalem.
10 Kada a faɗe shi a Gat; kada ma a yi kuka. A maimako haka, a yi birgima a cikin ƙura a Bet-Leyafra.
Do not be willing to announce it in Gath; may you not lament with tears. In the house of Dust, besprinkle yourselves with dust.
11 Ku wuce tsirara da kuma kunya, ku mazaunan Shafir. Bet-Ezel tana makoki domin babu wani daga Za’anan da ya fito don yă taimaka.
And cross over to your dwelling place, Beauty, bewildered by disgrace. She did not depart, who dwells at the place of departure. The House nearby, which remained firm by herself, will receive mourning from you.
12 Mazaunan Marot sun ƙosa su ga alheri, amma Ubangiji ya sauko da azaba, har zuwa ƙofar Urushalima.
For she has been weakened in goodness, who dwells in bitterness. For disaster has descended from the Lord to the gate of Jerusalem.
13 Ku da kuke zama a Lakish, ku ɗaura wa dawakai kekunan yaƙi. Gama ku kuka fara yin zunubi a Sihiyona, gama an sami laifofin Isra’ila a cikinku.
A tumult of four-horse chariots has stupefied the inhabitants of Lachish. The beginning has been sin for the daughter of Zion, because in you have been found the evil deeds of Israel.
14 Saboda haka za ku ba da kyautan bankwana ga Moreshet Gat. Garin Akzib zai zama abin yaudara ga sarakunan Isra’ila.
Because of this, she will send emissaries to the inheritance of Gath: the house of Lying in order to deceive the kings of Israel.
15 Ku mazaunan Maresha Ubangiji zai kawo wanda zai ci ku da yaƙi. Sarakunan Isra’ila za su gudu zuwa Adullam.
Nevertheless, I will lead an heir to you, who dwell in Mareshah: the glory of Israel will reach all the way to Adullam.
16 Ku aske kanku ƙwal don makoki, ku yi wa kanku ƙwalƙwal kamar ungulu. Gama za a ja’ya’yan da kuke farin ciki a kai su bauta.
Become bald and shaved for your delicate sons. Increase your baldness like the eagle. For they have been carried into captivity from you.

< Mika 1 >