< Mattiyu 1 >

1 Tarihin da aka rubuta game da asalin Yesu Kiristi ɗan Dawuda, ɗan Ibrahim.
Dette er forfedrene til Jesus Kristus, den lovede kongen, som var etterkommer til kong David og Abraham:
2 Ibrahim ya haifi Ishaku, Ishaku ya haifi Yaƙub, Yaƙub ya haifi Yahuda da’yan’uwansa,
Abraham, Isak og Jakob var far til Juda og brødrene hans. Videre fulgte:
3 Yahuda ya haifi Ferez da Zera, waɗanda Tamar ce mahaifiyarsu; Ferez ya haifi Hezron, Hezron ya haifi Ram,
Juda og Peres, som var tvillingbror til Serah, og moren het Tamar. Så kom: Hesron,
4 Ram ya haifi Amminadab, Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
Aram Amminadab, Naksjon,
5 Salmon ya haifi Bowaz, wanda Rahab ce mahaifiyarsa, Bowaz ya haifi Obed, wanda Rut ce mahaifiyarsa, Obed ya haifi Yesse,
Salmon, Boas, og moren het Rahab. Etterpå finner vi: Obed, og moren het Rut, Isai, som ble far til
6 Yesse kuwa ya haifi Sarki Dawuda. Dawuda ya haifi Solomon, wanda matar Uriya ce mahaifiyarsa.
kong David. Salomo, som var sønn til Batseba, enken etter Uria. Videre:
7 Solomon ya haifi Rehobowam, Rehobowam ya haifi Abiya, Abiya ya haifi Asa,
Rehabeam, Abia, Asaf,
8 Asa ya haifi Yehoshafat, Yehoshafat ya haifi Yehoram, Yehoram ya haifi Azariya,
Josafat, Joram, Ussia,
9 Azariya ya haifi Yotam, Yotam ya haifi Ahaz, Ahaz ya haifi Hezekiya,
Jotam, Akas, Hiskia,
10 Hezekiya ya haifi Manasse, Manasse ya haifi Amon, Amon ya haifi Yosiya,
Manasse, Amos,
11 Yosiya kuma ya haifi Yekoniya da’yan’uwansa a lokacin da aka kwashe su zuwa bauta a Babilon.
Josia, som var far til Jojakin og hans brødre, som ble født ved den tiden da folket ble ført bort til fangenskap i Babylon, og Jojakin.
12 Bayan an kwashe su zuwa bauta a Babilon. Yekoniya ya haifi Sheyaltiyel, Sheyaltiyel ya haifi Zerubbabel,
Etter å ha blitt ført bort til Babylon, fulgte: Sealtiel, Serubabel,
13 Zerubbabel ya haifi Abiyud, Abiyud ya haifi Eliyakim, Eliyakim ya haifi Azor,
Abiud, Eljakim, Asor,
14 Azor ya haifi Zadok, Zadok ya haifi Akim, Akim kuma ya haifi Eliyud,
Sadok, Akim, Eliud,
15 Eliyud ya haifi Eleyazar, Eleyazar ya haifi Mattan, Mattan ya haifi Yaƙub,
Eleasar, Mattan, Jakob,
16 Yaƙub ya haifi Yusuf, mijin Maryamu, wadda ta haifi Yesu, wanda ake kira Kiristi.
og Josef. Josef var mannen til Maria og hun var mor til Jesus Kristus.
17 Ta haka akwai zuriya goma sha huɗu ke nan duka-duka daga lokacin Ibrahim zuwa lokacin Dawuda, goma sha huɗu kuma daga Dawuda zuwa bauta a Babilon, goma sha huɗu kuma daga bauta a Babilon zuwa Kiristi.
Disse personene utgjør 14 slektledd fra Abraham og fram til kong David, 14 slektledd fra kong David og fram til tiden da jødene ble ført bort til Babylon og 14 slektledd fra epoken i Babylon og fram til Jesus Kristus.
18 Ga yadda haihuwar Yesu Kiristi ta kasance. An yi alkawarin auren mahaifiyarsa Maryamu, ga Yusuf. Amma tun kafin su zama miji da mata, sai aka tarar Maryamu tana da ciki, ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
Da Jesus Kristus ble født, gikk det slik til: Hans mor Maria var trolovet og skulle gifte seg med Josef. Men allerede før de var gift, ble hun med barn ved Guds Hellige Ånd.
19 Yusuf mijinta, da yake shi mai adalci ne, bai so yă ba ta kunya, yă tone mata asiri a fili ba, sai ya yi tunani yă sake ta a ɓoye.
Josef, hennes kommende mann, så da ingen annen utvei enn å skille seg fra henne i stillhet. Han ville leve etter Guds bud, men ønsket ikke å skjemme ut Maria offentlig.
20 Amma yana cikin wannan tunani, sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana masa cikin mafarki ya ce, “Yusuf ɗan Dawuda, kada ka ji tsoron ɗaukan Maryamu zuwa gidanka a matsayin matarka, gama cikin nan nata, daga wurin Ruhu Mai Tsarki ne.
Mens han fortsatt grublet på hvordan han skulle løse problemet, viste en Herrens engel seg for ham i en drøm. Engelen sa:”Josef, du som er etterkommer av kong David, du skal ikke nøle med å gifte deg med Maria, for det barnet hun bærer, er blitt til ved Guds Hellige Ånd.
21 Za tă haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu, gama shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”
Hun skal få en sønn, og du skal kalle ham Jesus, for han skal frelse folket sitt fra syndene deres.”
22 Duk wannan ya faru ne, don a cika abin da Ubangiji ya faɗi ta bakin annabin cewa,
På denne måten ble det som Gud hadde forutsagt ved profeten Jesaja, til virkelighet:
23 “Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, kuma za a kira shi Immanuwel” (wanda yake nufin “Allah tare da mu”).
”Lytt! Den unge jenta skal bli med barn og føde en sønn, og de skal kalle ham Immanuel, som betyr’Gud er med oss’.”
24 Da Yusuf ya farka daga barci, sai ya bi umarnin mala’ikan Ubangiji, ya ɗauki Maryamu zuwa gida a matsayin matarsa.
Da Josef våknet, gjorde han som engelen hadde gitt beskjed om, og han giftet seg med Maria.
25 Amma bai kwana da ita ba, sai bayan da ta haifi ɗan. Ya kuwa sa masa suna Yesu.
De hadde imidlertid ikke noe seksuelt samliv før sønnen var født. Josef ga ham navnet Jesus.

< Mattiyu 1 >