< Mattiyu 1 >

1 Tarihin da aka rubuta game da asalin Yesu Kiristi ɗan Dawuda, ɗan Ibrahim.
Sheshino ni shitabhu sha nndondonga gwa mena gwa lubheleko lwa a Yeshu Kilishitu bha ulongo gwa a Daudi, bha ulongo gwa a Bhulaimu, puyaaliji nnei.
2 Ibrahim ya haifi Ishaku, Ishaku ya haifi Yaƙub, Yaƙub ya haifi Yahuda da’yan’uwansa,
A Bhulaimu gubhankwete Ishaka, a Ishaka gubhankwete Yakobho, a Yakobho gubhankwete Yuda na ashaakulugwe na ashaapwakwe,
3 Yahuda ya haifi Ferez da Zera, waɗanda Tamar ce mahaifiyarsu; Ferez ya haifi Hezron, Hezron ya haifi Ram,
a Yuda gubhankwete Peleshi naka Shela anyinabhabhonji pubhashemwaga a Tamali, a Peleshi gubhankwete Eshiloni, a Eshiloni gubhankwete Lami.
4 Ram ya haifi Amminadab, Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
A Lami gubhankwete Aminadabhu. A Aminadabhu gubhankwete Nashoni, a Nashoni gubhankwete Shalomoni.
5 Salmon ya haifi Bowaz, wanda Rahab ce mahaifiyarsa, Bowaz ya haifi Obed, wanda Rut ce mahaifiyarsa, Obed ya haifi Yesse,
A Shalomoni gubhankwete Bhoashi, akwabhe Bhoashi pubhashemwaga a Laabhu, a Bhoashi gubhankwete Obhedi kwa akongobhabho a Luti, a Obhedi gubhankwete Yeshe,
6 Yesse kuwa ya haifi Sarki Dawuda. Dawuda ya haifi Solomon, wanda matar Uriya ce mahaifiyarsa.
Nabhalabho a Yeshe gubhankwete Mpalume Daudi. A Daudi gubhankwete Shelemani ku bhakongwe bhaliji akongobhabho a Ulia bhukala.
7 Solomon ya haifi Rehobowam, Rehobowam ya haifi Abiya, Abiya ya haifi Asa,
A Shelemani gubhankwete Leobhoamu, a Leobhoamu gubhankwete Abhiya, a Abhiya gubhankwete Ashapu,
8 Asa ya haifi Yehoshafat, Yehoshafat ya haifi Yehoram, Yehoram ya haifi Azariya,
A Ashapu gubhankwete Yoshepati, a Yoshepati gubhankwete Yolamu, a Yolamu gubhankwete Ushiya,
9 Azariya ya haifi Yotam, Yotam ya haifi Ahaz, Ahaz ya haifi Hezekiya,
a Ushiya gubhankwete Yoshamu, a Yoshamu gubhankwete Ashi, a Ashi gubhankwete Eshekia,
10 Hezekiya ya haifi Manasse, Manasse ya haifi Amon, Amon ya haifi Yosiya,
a Eshekia gubhankwete Manashe, a Manashe gubhankwete Amoni, a Amoni gubhankwete Yoshiya,
11 Yosiya kuma ya haifi Yekoniya da’yan’uwansa a lokacin da aka kwashe su zuwa bauta a Babilon.
a Yoshiya gubhankwete Yekoniya na ashaapwakwe, mobha Bhayaudi gubhapelekwenje ku Bhabhuloni.
12 Bayan an kwashe su zuwa bauta a Babilon. Yekoniya ya haifi Sheyaltiyel, Sheyaltiyel ya haifi Zerubbabel,
Bhayaudi bhakapelekwanjeje ku Bhabhuloni, a Yekoniya gubhankwete Sheatieli, a Sheatieli gubhankwete Shelubhabheli,
13 Zerubbabel ya haifi Abiyud, Abiyud ya haifi Eliyakim, Eliyakim ya haifi Azor,
a Shelubhabheli gubhankwete Abhiudi, a Abhiudi gubhankwete Eliakimu, a Eliakimu gubhankwete Asholi,
14 Azor ya haifi Zadok, Zadok ya haifi Akim, Akim kuma ya haifi Eliyud,
A Asholi gubhankwete Shadoki, a Shadoki gubhankwete Akimu, a Akimu gubhankwete Eliudi,
15 Eliyud ya haifi Eleyazar, Eleyazar ya haifi Mattan, Mattan ya haifi Yaƙub,
a Eliudi gubhankwete Eliashali, a Eliashali gubhankwete Matani, a Matani gubhankwete Yakobho,
16 Yaƙub ya haifi Yusuf, mijin Maryamu, wadda ta haifi Yesu, wanda ake kira Kiristi.
a Yakobho gubhaakwete a Yoshepu bhaaliji ambujebhabho a Malia, anyinabhabho a Yeshu bhaashemwa a Kilishitu.
17 Ta haka akwai zuriya goma sha huɗu ke nan duka-duka daga lokacin Ibrahim zuwa lokacin Dawuda, goma sha huɗu kuma daga Dawuda zuwa bauta a Babilon, goma sha huɗu kuma daga bauta a Babilon zuwa Kiristi.
Bhai puyaliji ibheleko likumi limo na nsheshe kutandubhila a Bhulaimu mpaka a Daudi na ibheleko likumi limo na nsheshe kutandubhila a Daudi mpaka pubhapelekwenje ku utumwa ku Bhabhuloni, na ibheleko likumi limo na nsheshe kutandubhila pubhapelekwenje ku utumwa ku Bhabhuloni mpaka pubhabhelekwe a Kilishitu.
18 Ga yadda haihuwar Yesu Kiristi ta kasance. An yi alkawarin auren mahaifiyarsa Maryamu, ga Yusuf. Amma tun kafin su zama miji da mata, sai aka tarar Maryamu tana da ciki, ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
Kubhelekwa kwa a Yeshu Kilishitu pukwaliji nnei, a Malia anyinabhabho a Yeshu, bhali muntemela na a Yoshepu, bhakanabhe gwabhala gubhaabhweni a Malia bhali na shitumbo kwa komboywa naka Mbumu jwa Ukonjelo.
19 Yusuf mijinta, da yake shi mai adalci ne, bai so yă ba ta kunya, yă tone mata asiri a fili ba, sai ya yi tunani yă sake ta a ɓoye.
Pabha a Yoshepu bhashinkubha bhanguja bhakapinjileje kutokomaya ntemela gwabho, kwa nneyo gubhapinjile kwaaleka kwa nng'iyo.
20 Amma yana cikin wannan tunani, sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana masa cikin mafarki ya ce, “Yusuf ɗan Dawuda, kada ka ji tsoron ɗaukan Maryamu zuwa gidanka a matsayin matarka, gama cikin nan nata, daga wurin Ruhu Mai Tsarki ne.
Bhali nkuganishiya genego, nnugono malaika jwa Bhakulungwa gwabhakoposhele nng'agamii alinkuti, “A Yoshepu bha ulongo gwa a Daudi, nnajogope kwaatola a Malia bhabhe akongobhenu, pabha Mbumu jwa Ukonjelo ni abhatendile bhabhe na shitumbo.
21 Za tă haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu, gama shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”
Shibhakole mwana jwannume, shimunsheme lina lyakwe Yeshu, pabha jwenejo apinga tapula bhandu bhakwe na yambi yabhonji.”
22 Duk wannan ya faru ne, don a cika abin da Ubangiji ya faɗi ta bakin annabin cewa,
Genego gashinkukoposhela nkupinga limalile lilobhe libhalugwile Bhakulungwa kuka nkulondola jwabho,
23 “Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, kuma za a kira shi Immanuwel” (wanda yake nufin “Allah tare da mu”).
“Nng'ishana shakole shitumbo, shankole mwana jwannume, shibhanshemanje lina lyakwe Manueli,” malombolelo gakwe, “A Nnungu pamo na uwe”.
24 Da Yusuf ya farka daga barci, sai ya bi umarnin mala’ikan Ubangiji, ya ɗauki Maryamu zuwa gida a matsayin matarsa.
Kwa nneyo, a Yoshepu bhakajumusheje gubhatendile malinga shibhalugulilwe naka malaika jula, gubhaatolile a Malia kubha akongobhabho.
25 Amma bai kwana da ita ba, sai bayan da ta haifi ɗan. Ya kuwa sa masa suna Yesu.
Bhakaamanyiji akongobhabho a Malia mpaka bhakankoleje mwana jwannume. Na a Yoshepu gubhanshemile lina lyakwe, Yeshu.

< Mattiyu 1 >