< Mattiyu 1 >

1 Tarihin da aka rubuta game da asalin Yesu Kiristi ɗan Dawuda, ɗan Ibrahim.
Ko te pukapuka o te whakapapa o Ihu Karaiti, tama a Rawiri, tama a Aperahama.
2 Ibrahim ya haifi Ishaku, Ishaku ya haifi Yaƙub, Yaƙub ya haifi Yahuda da’yan’uwansa,
Na ko ta Aperahama ko Ihaka; ta Ihaka ko Hakopa; ta Hakopa ko Hura ratou ko ona tuakana, ko ona teina;
3 Yahuda ya haifi Ferez da Zera, waɗanda Tamar ce mahaifiyarsu; Ferez ya haifi Hezron, Hezron ya haifi Ram,
Ta Hura raua ko Tamara ko Parete raua ko Hara; ta Parete ko Heteromo; ta Heteromo ko Arame;
4 Ram ya haifi Amminadab, Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
Ta Arame ko Aminarapa; ta Aminarapa ko Nahona; ta Nahona ko Haramono;
5 Salmon ya haifi Bowaz, wanda Rahab ce mahaifiyarsa, Bowaz ya haifi Obed, wanda Rut ce mahaifiyarsa, Obed ya haifi Yesse,
Ta Haramono raua ko Rahapa ko Poaha; ta Poaha raua ko Rutu ko Opere; ta Opere ko Hehe;
6 Yesse kuwa ya haifi Sarki Dawuda. Dawuda ya haifi Solomon, wanda matar Uriya ce mahaifiyarsa.
Ta Hehe ko Rawiri, ko te kingi; ta Rawiri kingi raua ko te wahine a Uria ko Horomona;
7 Solomon ya haifi Rehobowam, Rehobowam ya haifi Abiya, Abiya ya haifi Asa,
Ta Horomona ko Rehopoama; ta Rehopoama ko Apia; ta Apia ko Aha;
8 Asa ya haifi Yehoshafat, Yehoshafat ya haifi Yehoram, Yehoram ya haifi Azariya,
Ta Aha ko Iehohapata; ta Iehohapata ko Iorama; ta Iorama ko Ohiaha;
9 Azariya ya haifi Yotam, Yotam ya haifi Ahaz, Ahaz ya haifi Hezekiya,
Ta Ohiaha ko Iotama; ta Iotama ko Ahata; ta Ahata ko Hetekia;
10 Hezekiya ya haifi Manasse, Manasse ya haifi Amon, Amon ya haifi Yosiya,
Ta Hetekia ko Manahi; ta Manahi ko Amono; ta Amono ko Hohia;
11 Yosiya kuma ya haifi Yekoniya da’yan’uwansa a lokacin da aka kwashe su zuwa bauta a Babilon.
Ta Hohia ko Hekonia ratou ko ona teina; i te wa o te whakahekenga ki Papurona:
12 Bayan an kwashe su zuwa bauta a Babilon. Yekoniya ya haifi Sheyaltiyel, Sheyaltiyel ya haifi Zerubbabel,
A, i muri i te whakahekenga atu ki Papurona, ka whanau ta Hekonia ko Haratiera; ta Haratiera ko Herupapera;
13 Zerubbabel ya haifi Abiyud, Abiyud ya haifi Eliyakim, Eliyakim ya haifi Azor,
Ta Herupapera ko Apiuru; ta Apiuru ko Eriakimi; ta Eriakimi ko Atoro;
14 Azor ya haifi Zadok, Zadok ya haifi Akim, Akim kuma ya haifi Eliyud,
Ta Atoro ko Haroko; ta Haroko ko Akimi; ta Akimi ko Eriuru;
15 Eliyud ya haifi Eleyazar, Eleyazar ya haifi Mattan, Mattan ya haifi Yaƙub,
Ta Eriuru ko Ereatara; ta Ereatara ko Matana; ta Matana ko Hakopa;
16 Yaƙub ya haifi Yusuf, mijin Maryamu, wadda ta haifi Yesu, wanda ake kira Kiristi.
Ta Hakopa ko Hohepa, ko te tahu a Meri; whanau ake ta Meri ko Ihu, e kiia nei ko te Karaiti.
17 Ta haka akwai zuriya goma sha huɗu ke nan duka-duka daga lokacin Ibrahim zuwa lokacin Dawuda, goma sha huɗu kuma daga Dawuda zuwa bauta a Babilon, goma sha huɗu kuma daga bauta a Babilon zuwa Kiristi.
Heoi, ko nga whakatupuranga katoa o Aperahama tae noa ki a Rawiri tekau ma wha nga whakatupuranga; o Rawiri tae noa ki te whakahekenga ki Papurona tekau ma wha nga whakatupuranga; a no te whakahekenga ki Papurona tae noa ki a te Karaiti tekau ma wha nga whakatupuranga.
18 Ga yadda haihuwar Yesu Kiristi ta kasance. An yi alkawarin auren mahaifiyarsa Maryamu, ga Yusuf. Amma tun kafin su zama miji da mata, sai aka tarar Maryamu tana da ciki, ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
Na ko te whanautanga tenei o Ihu Karaiti: he mea taumau a Meri, tona whaea, ma Hohepa, a i te mea kiano raua i tata noa ki a raua, ka kitea kua hapu ia i te Wairua Tapu.
19 Yusuf mijinta, da yake shi mai adalci ne, bai so yă ba ta kunya, yă tone mata asiri a fili ba, sai ya yi tunani yă sake ta a ɓoye.
Otira he tangata tika tana tahu, a Hohepa, a kahore ona ngakau kia whakakitea nuitia ia, ka mea kia whakarerea pukutia.
20 Amma yana cikin wannan tunani, sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana masa cikin mafarki ya ce, “Yusuf ɗan Dawuda, kada ka ji tsoron ɗaukan Maryamu zuwa gidanka a matsayin matarka, gama cikin nan nata, daga wurin Ruhu Mai Tsarki ne.
Otiia i a ia e hurihuri ana i enei mea, na, ka puta moemoea mai tetahi anahera a te Ariki ki a ia, ka mea, E Hohepa, e te tama a Rawiri, kaua e hopohopo ki te tango i a Meri, i tau wahine; na te Wairua Tapu hoki tona hapu.
21 Za tă haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu, gama shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”
A e whanau ia he tama, me hua e koe tona ingoa ko IHU: no te mea mana e whakaora tona iwi i o ratou hara.
22 Duk wannan ya faru ne, don a cika abin da Ubangiji ya faɗi ta bakin annabin cewa,
Na ka oti tenei katoa, katahi ka rite ta te Ariki, i korerotia e te poropiti, i mea ai ia,
23 “Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, kuma za a kira shi Immanuwel” (wanda yake nufin “Allah tare da mu”).
Na, ka hapu te wahine, ka whanau hoki he tama, a ka huaina e ratou tona ingoa ko Emanuera, ko tona whakamaoritanga tenei, Kei a tatou te Atua.
24 Da Yusuf ya farka daga barci, sai ya bi umarnin mala’ikan Ubangiji, ya ɗauki Maryamu zuwa gida a matsayin matarsa.
A ka ara ake a Hohepa i te moe, ka meatia e ia ta te anahera a te Ariki i whakahau ai ki a ia, a tango ana ia i tana wahine:
25 Amma bai kwana da ita ba, sai bayan da ta haifi ɗan. Ya kuwa sa masa suna Yesu.
A kihai i mohio ki a ia, whanau noa tana tama matamua: a huaina ana e ia tona ingoa ko IHU.

< Mattiyu 1 >