< Mattiyu 1 >

1 Tarihin da aka rubuta game da asalin Yesu Kiristi ɗan Dawuda, ɗan Ibrahim.
Echitabho cho luganda lwa Yesu Kristo omwana wa Daudi omwana wa
2 Ibrahim ya haifi Ishaku, Ishaku ya haifi Yaƙub, Yaƙub ya haifi Yahuda da’yan’uwansa,
Ibrahimu; Ibrahimu aliga esemwene Isaka na Isaka esemwene Yakobo na Yakobo alisemwene Yuda na bhamula bhabho.
3 Yahuda ya haifi Ferez da Zera, waɗanda Tamar ce mahaifiyarsu; Ferez ya haifi Hezron, Hezron ya haifi Ram,
Yuda aliga ali esemwene Peresi na Sera ku Tamari Peresi ali esemwene waHezroni na Hezroni ali esemwene wa Ramu,
4 Ram ya haifi Amminadab, Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
Ramu aliga ali semwene Aminadabu. Aminadabu alisemwene Nashoni. Nashoni alisemwene Salimoni.
5 Salmon ya haifi Bowaz, wanda Rahab ce mahaifiyarsa, Bowaz ya haifi Obed, wanda Rut ce mahaifiyarsa, Obed ya haifi Yesse,
Salimoni alisemwene wa Boazi ku Rahabu, Bohazi alisemwene wa Obedi ku Ruth, Obedi alisemwene Yese.
6 Yesse kuwa ya haifi Sarki Dawuda. Dawuda ya haifi Solomon, wanda matar Uriya ce mahaifiyarsa.
Yese alisemwene omkama Daudi. Daudi aliga alisemwene Selemani ku mugasi wa Huria.
7 Solomon ya haifi Rehobowam, Rehobowam ya haifi Abiya, Abiya ya haifi Asa,
. Sulemani aliga alisemwene Rehoboamu, Rehobohamu alisemwene wa Abiya, Abiya alisemwene wa Asa.
8 Asa ya haifi Yehoshafat, Yehoshafat ya haifi Yehoram, Yehoram ya haifi Azariya,
Asa aliga alisemwene wa Yehoshafati, Yehoshafati alisemwene wa Yoramu, na Yoramu alisemwene wa Uzia.
9 Azariya ya haifi Yotam, Yotam ya haifi Ahaz, Ahaz ya haifi Hezekiya,
Uzia aliga alisemwene wa Yothamu, Yothamu alisemwene wa Ahazi, Ahazi alisemwene wa Hezekia.
10 Hezekiya ya haifi Manasse, Manasse ya haifi Amon, Amon ya haifi Yosiya,
Hezekia aliga alisemwene wa Manase, Manase alisemwene wa Amoni na Amoni alisemwene Yosia
11 Yosiya kuma ya haifi Yekoniya da’yan’uwansa a lokacin da aka kwashe su zuwa bauta a Babilon.
Yosia aligaesemwene Yekonia na bhamula bhabho omwanya gunu bhagegelwe okusilwa Babeli.
12 Bayan an kwashe su zuwa bauta a Babilon. Yekoniya ya haifi Sheyaltiyel, Sheyaltiyel ya haifi Zerubbabel,
Omwanya gunu bhaliga bhamalile ogegwa okuja Babeli, Yekonia aliga alisemwene Shatieri, Shatieri aliga ali jaji wabhona Zelubabeli.
13 Zerubbabel ya haifi Abiyud, Abiyud ya haifi Eliyakim, Eliyakim ya haifi Azor,
Zerubabeli aliga alisemwene Abiudi, Abiudi alisemwene wa Eliakimu, na Eliakimu ali semwene wa Azori.
14 Azor ya haifi Zadok, Zadok ya haifi Akim, Akim kuma ya haifi Eliyud,
Azori aliga alisemwene Zadoki, Zadoki alisemwene Akimu, na Akimu alisemwene Eliudi.
15 Eliyud ya haifi Eleyazar, Eleyazar ya haifi Mattan, Mattan ya haifi Yaƙub,
Eliudi aliga alisemwene Elieza, Elieza ali esemwene Matani na Matani alisemwene Yakobo.
16 Yaƙub ya haifi Yusuf, mijin Maryamu, wadda ta haifi Yesu, wanda ake kira Kiristi.
Yakobo aliga alisemwene Yusufu omulume wa Mariamu unu kusoka kumwene Yesu ebhuhye unu katogwa Kristo.
17 Ta haka akwai zuriya goma sha huɗu ke nan duka-duka daga lokacin Ibrahim zuwa lokacin Dawuda, goma sha huɗu kuma daga Dawuda zuwa bauta a Babilon, goma sha huɗu kuma daga bauta a Babilon zuwa Kiristi.
Jinyibhulo jona okusoka ku Ibrahimu okukinga ku Daudi jaliga nyibhulo ekumi nena, okusoka ku Daudi okukinga okugegwa okuja Babeli ni nyibhulo ekumi nena, no kusoka anu bhagegibhwe okuja Babeli okukinga ku Kristo ni nyibhulo ekumi nena.
18 Ga yadda haihuwar Yesu Kiristi ta kasance. An yi alkawarin auren mahaifiyarsa Maryamu, ga Yusuf. Amma tun kafin su zama miji da mata, sai aka tarar Maryamu tana da ciki, ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
Okwibhulwa kwa Yesu Kristo kwaliga kulikutya, nyila wae, Mariamu aliga nasandwa na Yusufu, akatungu bhachali kubhonana chi mubhili nabhonekana ati alinainda kubhutulo bhwo mwoyo mwelu.
19 Yusuf mijinta, da yake shi mai adalci ne, bai so yă ba ta kunya, yă tone mata asiri a fili ba, sai ya yi tunani yă sake ta a ɓoye.
Omulume wae Yusufu aliga munu mulengelesi atendele kumuswasha abhwelu. Alamuye okubhusiga obhuko obhwo kwo bhwitebhe.
20 Amma yana cikin wannan tunani, sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana masa cikin mafarki ya ce, “Yusuf ɗan Dawuda, kada ka ji tsoron ɗaukan Maryamu zuwa gidanka a matsayin matarka, gama cikin nan nata, daga wurin Ruhu Mai Tsarki ne.
Anu aliga acheganilisha ingulu ya magambo ago, Maraika wa Nyamuanga namubhonekela mu chiloto naika, Yusufu mwende Daudi utajakubhaya okumugega Mariamu kuti mugasi wao kulwokubha inda inu alinayo ni kulwo bhuturo bhwo Mwoyo mweru.
21 Za tă haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu, gama shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”
Kaja okwibhula omwana we chilume umubhilikile lisina lyae Yesu, kulwokubha niwe kaja okubhachungula abhanu bhae ne bhibhibhi byebwe
22 Duk wannan ya faru ne, don a cika abin da Ubangiji ya faɗi ta bakin annabin cewa,
Gona ganu gasokana okukumisha jinu jaikilwe na Nyamuanga ku njila yo mulagi naika,
23 “Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, kuma za a kira shi Immanuwel” (wanda yake nufin “Allah tare da mu”).
Lola omuyala aligega inda no kwibhula omwana mulume na bhalimubhilikila lisina lyae Imanuel insonga yendemo Nyamuanga amwi neswe.
24 Da Yusuf ya farka daga barci, sai ya bi umarnin mala’ikan Ubangiji, ya ɗauki Maryamu zuwa gida a matsayin matarsa.
Yusufu emukile okusoka muntilo nakola kutyo Malaika wa Nyamuanga kutyo amulagilie na amugegele kuti mugasi wae.
25 Amma bai kwana da ita ba, sai bayan da ta haifi ɗan. Ya kuwa sa masa suna Yesu.
Kulwejo nolo jabhee kutyo atamamile nage katungu kone okukinga ao ebhulie omwana we chilume namubhilikila lisina lyae Yesu.

< Mattiyu 1 >