< Mattiyu 1 >

1 Tarihin da aka rubuta game da asalin Yesu Kiristi ɗan Dawuda, ɗan Ibrahim.
Table généalogique de Jésus-Christ, fils de David, fils d'Abraham
2 Ibrahim ya haifi Ishaku, Ishaku ya haifi Yaƙub, Yaƙub ya haifi Yahuda da’yan’uwansa,
Abraham engendra Isaac; Isaac engendra Jacob; Jacob engendra Juda et ses frères;
3 Yahuda ya haifi Ferez da Zera, waɗanda Tamar ce mahaifiyarsu; Ferez ya haifi Hezron, Hezron ya haifi Ram,
Juda engendra Pharès et Zara qu’il eut de Thamar; Pharès engendra Esrôm; Esrôm engendra Aram;
4 Ram ya haifi Amminadab, Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
Aram engendra Aminadab; Aminadab engendra Naasson; Naasson engendra Salmon;
5 Salmon ya haifi Bowaz, wanda Rahab ce mahaifiyarsa, Bowaz ya haifi Obed, wanda Rut ce mahaifiyarsa, Obed ya haifi Yesse,
Salmon engendra Boès, qu'il eut de Rachab; Boès engendra Jobed, qu'il eut de Ruth; Jobed engendra Jessaï;
6 Yesse kuwa ya haifi Sarki Dawuda. Dawuda ya haifi Solomon, wanda matar Uriya ce mahaifiyarsa.
Jessaï engendra David, le roi David engendra Salomon, qu’il eut de la femme d'Urie;
7 Solomon ya haifi Rehobowam, Rehobowam ya haifi Abiya, Abiya ya haifi Asa,
Salomon engendra Roboam; Roboam engendra Abia; Abia engendra Asaph;
8 Asa ya haifi Yehoshafat, Yehoshafat ya haifi Yehoram, Yehoram ya haifi Azariya,
Asaph engendra Josaphat; Josaphat engendra Joram; Joram engendra Ozeia;
9 Azariya ya haifi Yotam, Yotam ya haifi Ahaz, Ahaz ya haifi Hezekiya,
Ozeia engendra Joatham; Joatham engendra Achaz; Achaz engendra Ezéchias;
10 Hezekiya ya haifi Manasse, Manasse ya haifi Amon, Amon ya haifi Yosiya,
Ezéchias engendra Manassé; Manassé engendra Amon; Amon engendra Josias;
11 Yosiya kuma ya haifi Yekoniya da’yan’uwansa a lokacin da aka kwashe su zuwa bauta a Babilon.
Josias engendra Jéchonias et ses frères (c'était au temps de la déportation à Babylone).
12 Bayan an kwashe su zuwa bauta a Babilon. Yekoniya ya haifi Sheyaltiyel, Sheyaltiyel ya haifi Zerubbabel,
Après la déportation à Babylone: Jéchonias engendra Salathiel; Salathiel engendra Zorobabel;
13 Zerubbabel ya haifi Abiyud, Abiyud ya haifi Eliyakim, Eliyakim ya haifi Azor,
Zorobabel engendra Abioud; Abioud engendra Eliakeïm; Eliakeïm engendra Azôr;
14 Azor ya haifi Zadok, Zadok ya haifi Akim, Akim kuma ya haifi Eliyud,
Azôr engendra Sadok; Sadok engendra Acheïm; Acheïm engendra Elioud;
15 Eliyud ya haifi Eleyazar, Eleyazar ya haifi Mattan, Mattan ya haifi Yaƙub,
Elioud engendra Eléazar; Eléazar engendra Matthan; Matthan engendra Jacob;
16 Yaƙub ya haifi Yusuf, mijin Maryamu, wadda ta haifi Yesu, wanda ake kira Kiristi.
Jacob engendra Joseph, l'époux de Marie, de laquelle est né Jésus, dit le Christ.
17 Ta haka akwai zuriya goma sha huɗu ke nan duka-duka daga lokacin Ibrahim zuwa lokacin Dawuda, goma sha huɗu kuma daga Dawuda zuwa bauta a Babilon, goma sha huɗu kuma daga bauta a Babilon zuwa Kiristi.
En tout donc, d'Abraham jusqu'à David: quatorze générations. — De David jusqu'à la déportation à Babylone: quatorze générations. — De la déportation à Babylone jusqu'au Christ: quatorze générations.
18 Ga yadda haihuwar Yesu Kiristi ta kasance. An yi alkawarin auren mahaifiyarsa Maryamu, ga Yusuf. Amma tun kafin su zama miji da mata, sai aka tarar Maryamu tana da ciki, ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
Voici comment Jésus-Christ vint au monde: Marie, sa mère, après avoir été fiancée à Joseph et avant qu'ils eussent vécu ensemble, se trouva enceinte par l'Esprit saint.
19 Yusuf mijinta, da yake shi mai adalci ne, bai so yă ba ta kunya, yă tone mata asiri a fili ba, sai ya yi tunani yă sake ta a ɓoye.
Or Joseph, son mari, était un juste. Ne voulant pas lui faire affront, il résolut de rompre avec elle sans bruits.
20 Amma yana cikin wannan tunani, sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana masa cikin mafarki ya ce, “Yusuf ɗan Dawuda, kada ka ji tsoron ɗaukan Maryamu zuwa gidanka a matsayin matarka, gama cikin nan nata, daga wurin Ruhu Mai Tsarki ne.
Comme il était en cette pensée, un ange du Seigneur lui apparut en songe et lui dit: «Joseph, fils de David, n'hésite pas à recevoir chez toi, ta femme, Marie, car ce qu'elle a conçu est de l'Esprit saint.
21 Za tă haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu, gama shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”
Elle mettra un fils au monde et tu lui donneras le nom de Jésus; c'est lui, en effet, qui sauvera son peuple de ses péchés.»
22 Duk wannan ya faru ne, don a cika abin da Ubangiji ya faɗi ta bakin annabin cewa,
(Or tout cela arriva afin que fût accompli ce que le Seigneur avait dit par le prophète en ces mots:
23 “Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, kuma za a kira shi Immanuwel” (wanda yake nufin “Allah tare da mu”).
«Voici la vierge sera enceinte; elle mettra un fils au monde; Et on lui donnera le nom d'Emmanuel» ce qui signifie: Dieu avec nous.)
24 Da Yusuf ya farka daga barci, sai ya bi umarnin mala’ikan Ubangiji, ya ɗauki Maryamu zuwa gida a matsayin matarsa.
Joseph, à son réveil, agit d'après les ordres de l'ange du Seigneur: il reçut sa femme chez lui;
25 Amma bai kwana da ita ba, sai bayan da ta haifi ɗan. Ya kuwa sa masa suna Yesu.
et il ne la connut point avant qu'elle eût mis au monde un fils auquel il donna le nom de Jésus.

< Mattiyu 1 >