< Mattiyu 8 >

1 Da ya sauko daga dutsen, sai taron mutane mai yawan gaske suka bi shi.
When he had come down from the mountain, great multitudes followed him.
2 Wani mutum mai kuturta ya zo ya durƙusa a gabansa ya ce, “Ubangiji, in kana so, kana iya tsabtacce ni.”
And lo! there came a leper and bowed down before him, saying, Lord, if thou wilt, thou canst cleanse me.
3 Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin. Ya ce, “Ina so, ka tsabtacce!” Nan da nan aka warkar da shi daga kuturtarsa.
And he put forth his hand, and touched him, saying, I will; be thou cleansed. And immediately his leprosy was cleansed.
4 Sai Yesu ya ce masa, “Ka lura kada ka gaya wa kowa. Sai dai ka tafi, ka nuna kanka ga firist ka kuma yi bayarwar da Musa ya umarta, a matsayin shaida gare su.”
And Jesus saith to him, See thou tell no one; but go, show thyself to the priest, and offer the gift that Moses commanded, for a testimony to them.
5 Da Yesu ya shiga Kafarnahum, sai wani jarumi ya zo wurinsa, yana neman taimako.
And when he had entered into Capernaum, there came to him a centurion, beseeching him,
6 Ya ce, “Ubangiji, bawana yana kwance a gida shanyayye, yana kuma shan azaba ƙwarai.”
and saying, Lord, my servant lieth at home palsied, sorely tormented.
7 Yesu ya ce masa, “Zan je in warkar da shi.”
He saith to him, I will come and heal him.
8 Jarumin ya amsa, “Ubangiji, ban cancanci in sa ka zo gidana ba, ka dai yi magana kawai, bawana zai warke.
But the centurion answered and said, Lord, I am not worthy that thou shouldst come under my roof; but only command with a word, and my servant will be made well.
9 Gama ni kaina mutum ne a ƙarƙashin iko, da kuma sojoji a ƙarƙashina. Nakan ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai yă tafi; wancan kuma, ‘Zo nan,’ sai yă zo. Nakan ce wa bawana, ‘Yi wannan,’ sai kuwa yă yi.”
For even I am a man under authority, having soldiers under me; and I say to this one, Go, and he goeth; and to another, Come, and he cometh; and to my servant, Do this, and he doeth it.
10 Da Yesu ya ji wannan, sai ya yi mamaki ya kuma ce wa waɗanda suke binsa, “Gaskiya nake gaya muku, ban taɓa samun wani a Isra’ila da bangaskiya mai girma haka ba.
When Jesus heard this, he marveled, and said to those who followed, Truly do I say to you, Not even in Israel have I found such faith.
11 Ina kuma gaya muku da yawa za su zo daga gabas da kuma yamma, su ɗauki wuraren zamansu a biki tare da Ibrahim, Ishaku, da Yaƙub a cikin mulkin sama.
And I say to you, that many will come from the east and the west, and recline at table with Abraham and Isaac and Jacob in the kingdom of heaven.
12 Amma za a jefar da’ya’yan mulki waje, zuwa cikin baƙin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.”
But the sons of the kingdom will go out into the outer darkness; there will be wailing and gnashing of teeth.
13 Sa’an nan Yesu ya ce wa jarumin, “Je ka! Za a yi bisa ga bangaskiyarka.” A daidai wannan lokaci bawansa kuwa ya warke.
And Jesus said to the centurion, Go thy way; as thou hast believed, so be it done to thee. And the servant was made well in that hour.
14 Da Yesu ya zo cikin gidan Bitrus, sai ya ga surukar Bitrus tana kwance a gado tana da zazzaɓi.
And when Jesus had come into Peter's house, he saw his wife's mother lying sick of a fever.
15 Ya taɓa hannunta sai zazzaɓin ya sake ta, ta kuwa tashi ta fara yin masa hidima.
And he touched her hand, and the fever left her; and she arose, and waited on him.
16 Da yamma ta yi, aka kawo masa masu aljanu da yawa, ya kuwa fitar da ruhohin ta wurin magana, ya kuma warkar da dukan marasa lafiya.
And when evening came, they brought to him many that were possessed by demons; and he cast out the spirits with a word, and healed all that were sick;
17 Wannan ya faru ne domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa, “Ya ɗebi rashin lafiyarmu, ya kuma ɗauki cututtukanmu.”
that it might be fulfilled which was spoken through Isaiah the prophet, saying, “He himself took our infirmities, and bore our diseases.”
18 Da Yesu ya ga taron mutane kewaye da shi, sai ya ba da umarni a ƙetare zuwa ɗayan hayin tafkin.
And Jesus, seeing great multitudes about him, gave orders to depart to the other side.
19 Sai wani malamin dokoki ya zo wurinsa ya ce, “Malam, zan bi ka duk inda za ka.”
And a certain scribe came and said to him, Teacher, I will follow thee wherever thou goest.
20 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”
And Jesus saith to him, The foxes have holes, and the birds of the air have lodging-places; but the Son of man hath not where to lay his head.
21 Sai wani almajiri ya ce masa, “Ubangiji, da farko bari in je in binne mahaifina.”
And another of the disciples said to him, Lord, suffer me first to go and bury my father.
22 Amma Yesu ya ce masa, “Ka bi ni, ka bar matattu su binne matattunsu.”
But he saith to him, Follow me, and let the dead bury their own dead.
23 Sai ya shiga jirgin ruwa, almajiransa kuwa suka bi shi.
And when he had gone on board the boat, his disciples followed him.
24 Ba zato ba tsammani, sai wani babban hadari ya taso a tafkin, har raƙuman ruwan suka sha kan jirgin. Amma Yesu yana barci.
And, lo! a great tempest arose on the lake, so that the boat was almost covered by the waves; but he was sleeping.
25 Almajiran suka je suka tashe shi, suna cewa, “Ubangiji, ka cece mu! Za mu nutse!”
And they came and awoke him, saying, Lord, save! we are perishing.
26 Ya amsa ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, me ya sa kuke tsoro haka?” Sa’an nan ya tashi ya tsawata wa iskar da kuma raƙuman ruwan, sai wuri ya yi tsit gaba ɗaya.
And he saith to them, Why are ye fearful, ye of little faith? Then he arose, and rebuked the winds and the waves; and there was a great calm.
27 Mutanen suka yi mamaki suka ce, “Wane irin mutum ne wannan? Har iska da raƙuman ruwa suna masa biyayya!”
And the men marveled, saying, What manner of man is this, that even the winds and the waves obey him?
28 Da ya isa ɗayan gefen a yankin Gadarenawa (ko kuwa Gerasenawa), sai ga mutum biyu masu aljanu suna fitowa daga kaburbura suka tarye shi. Su abin tsoro ne ƙwarai, har ba mai iya bin wannan hanya.
And when he had come to the other side, into the country of the Gadarenes, there met him two men possessed by demons, coming out of the tombs, exceedingly fierce, so that no one could pass by that way.
29 Suka yi ihu suka ce, “Me ya haɗa ka da mu, Ɗan Allah?” Ka zo ne nan don ka ji mana kafin lokaci yă yi?
And lo! they cried out, saying, What have we to do with thee, Son of God? Didst thou come here to torment us before the time?
30 Nesa kaɗan da su kuwa akwai babban garken aladu da yake kiwo.
Now there was at a distance from them a herd of many swine feeding.
31 Aljanun suka roƙi Yesu suka ce, “In ka fitar da mu, tura mu cikin garken aladun nan.”
And the demons besought him, saying, If thou cast us out, send us into the herd of swine.
32 Ya ce musu, “Ku tafi!” Sai suka fita suka shiga cikin aladun, dukan garken kuwa ya gangara a guje daga kan tudun zuwa cikin tafkin aladun kuma suka mutu a cikin ruwa.
And he said to them, Go. And they came out, and went into the swine. And lo! the whole herd rushed down the steep into the lake, and perished in the waters.
33 Masu kiwon aladun suka ruga, suka je cikin gari suka ba da labarin dukan wannan, haɗe da abin da ya faru da mutanen nan masu aljanu.
And the herdsmen fled, and went away into the city, and told everything, and what had happened to the men possessed by demons.
34 Sai dukan garin suka fito don su taryi Yesu. Da suka kuwa gan shi, sai suka roƙe shi yă bar musu yanki.
And lo! the whole city came out to meet Jesus; and when they saw him, they besought him to depart from their borders.

< Mattiyu 8 >