< Mattiyu 7 >

1 “Kada ku ba wa kowa laifi, don kada a ba ku laifi ku ma.
Judge not, that ye be not judged.
2 Gama da irin shari’ar da kuka yi wa waɗansu, da ita za a shari’anta ku. Mudun da kuka yi awo da shi, da shi za a yi muku.
For with what judgment ye judge, ye shall be judged: and with the measure which ye measure with, it shall be measured to you again.
3 “Don me kake duban ɗan tsinken da yake idon ɗan’uwanka, alhali kuwa ga gungume a naka ido?
And why beholdest thou the mote that is in thy brother’s eye, but considerest not the beam that is in thy own eye?
4 Yaya za ka ce wa ɗan’uwanka, ‘Bari in cire maka ɗan tsinken nan daga idonka,’ alhali kuwa a kowane lokaci akwai gungume a naka ido?
Or how wilt thou say to thy brother, Let me pull out the mote out of thy eye; and, behold, a beam is in thy own eye?
5 Kai munafuki, fara cire gungumen da yake idonka, a sa’an nan ne za ka iya gani sosai yadda za ka cire ɗan tsinken da yake a idon ɗan’uwanka.
Thou hypocrite, first cast out the beam out of thy own eye; and then shalt thou see clearly to cast out the mote out of thy brother’s eye.
6 “Kada ku ba karnuka abin da yake mai tsarki; kada kuma ku jefa wa aladu lu’ulu’anku. In kuka yi haka za su tattake su, sa’an nan su juyo su jijji muku ciwo.
Give not that which is holy to dogs, neither cast ye your pearls before swine, lest they trample them under their feet, and turn again and rend you.
7 “Ku roƙa za a ba ku; ku nema za ku samu; ku ƙwanƙwasa za a kuwa buɗe muku ƙofa.
Ask, and it shall be given you; seek, and ye shall find; knock, and it shall be opened to you:
8 Gama duk wanda ya roƙa, akan ba shi; wanda ya nema kuwa, yakan samu, wanda kuma ya ƙwanƙwasa, za a buɗe masa ƙofa.
For every one that asketh receiveth; and he that seeketh findeth; and to him that knocketh it shall be opened.
9 “Wane ne a cikinku in ɗansa ya roƙe shi burodi, sai yă ba shi dutse?
Or what man is there of you, who if his son shall ask bread, will give him a stone?
10 Ko kuwa in ya roƙe shi kifi, sai yă ba shi maciji?
Or if he shall ask a fish, will he give him a serpent?
11 In ku da kuke mugaye kun san yadda za ku ba da kyautai masu kyau ga’ya’yanku, balle Ubanku na sama, ba zai fi ku iya ba da abubuwa masu kyau, ga su waɗanda suka roƙe shi ba!
If ye then, being evil, know how to give good gifts to your children, how much more shall your Father who is in heaven give good things to them that ask him?
12 Saboda haka, duk abin da kuke so mutane su yi muku, ku ma sai ku yi musu, domin wannan shi ne Doka da koyarwar Annabawa sun ƙunsa.
Therefore all things whatever ye would that men should do to you, do ye even so to them: for this is the law and the prophets.
13 “Ku shiga ta matsattsiyar ƙofa. Gama ƙofar zuwa hallaka faɗaɗɗiya ce mai sauƙin bi kuma, masu shiga ta cikinta kuwa suna da yawa.
Enter ye in at the narrow gate: for wide is the gate, and broad is the way, that leadeth to destruction, and many there are who go in by it:
14 Amma ƙofar zuwa rai, ƙarama ce matsattsiya kuma, masu samunta kuwa kaɗan ne.
Because small is the gate, and narrow is the way, which leadeth to life, and few there are that find it.
15 “Ku yi hankali da annabawan ƙarya. Sukan zo muku da kamannin tumaki, amma daga ciki mugayen kyarketai ne.
Beware of false prophets, who come to you in sheep’s clothing, but inwardly they are ravening wolves.
16 Ta wurin aikinsu za ku gane su. Mutane suna iya tsinkan inabi a jikin ƙaya, ko kuwa ɓaure a jikin sarƙaƙƙiya?
Ye shall know them by their fruits. Do men gather grapes from thorns, or figs from thistles?
17 Haka ma kowane itace mai kyau yakan ba da’ya’ya masu kyau, kuma mummunan itace ba ya ba da’ya’ya masu kyau.
Even so every good tree bringeth forth good fruit; but a corrupt tree bringeth forth bad fruit.
18 Itace mai kyau ba ya ba da munanan’ya’ya, haka kuma mummunan itace ba ya ba da’ya’ya masu kyau.
A good tree cannot bring forth bad fruit, neither can a corrupt tree bring forth good fruit.
19 Duk itacen da ba ya ba da’ya’ya masu kyau sai a sare shi a jefa cikin wuta.
Every tree that bringeth not forth good fruit is hewn down, and cast into the fire.
20 Ta haka, ta wurin aikinsu za ku gane su.”
Therefore by their fruits ye shall know them.
21 “Ba duk mai ce mini, ‘Ubangiji, Ubangiji,’ ne zai shiga mulkin sama ba, sai dai wanda yake aikata nufin Ubana da yake sama.
Not every one that saith to me, Lord, Lord, shall enter into the kingdom of heaven; but he that doeth the will of my Father who is in heaven.
22 Da yawa za su ce mini a wannan rana, ‘Ubangiji, Ubangiji, ashe, ba mu yi annabci a cikin sunanka ba, ba kuma a cikin sunanka ne muka fitar da aljanu, muka yi abubuwan banmamaki da yawa ba?’
Many will say to me in that day, Lord, Lord, have we not prophesied in thy name? and in thy name have cast out demons? and in thy name done many wonderful works?
23 Sa’an nan zan ce musu a fili, ‘Ban taɓa saninku ba. Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta!’
And then will I profess to them, I never knew you: depart from me, ye that work iniquity.
24 “Saboda haka duk wanda yake jin kalmomin nan nawa yake kuma aikata su, yana kama da mutum mai hikima wanda ya gina gidansa a kan dutse.
Therefore whoever heareth these sayings of mine, and doeth them, I will liken him to a wise man, who built his house upon a rock:
25 Ruwan sama ya sauko, rafuffuka suka cika, iska kuma ta hura ta bugi gidan; duk da haka bai fāɗi ba, gama yana da harsashinsa a kan dutse.
And the rain descended, and the floods came, and the winds blew, and beat upon that house; and it fell not: for it was founded upon a rock.
26 Amma duk wanda yake jin kalmomin nan nawa bai kuwa aikata su ba, yana kama da wani wawa wanda ya gina gidansa a kan yashi.
And every one that heareth these sayings of mine, and doeth them not, shall be likened to a foolish man, who built his house upon the sand:
27 Ruwan sama ya sauko, rafuffuka suka cika, iska kuwa ta hura ta bugi gidan, sai ya fāɗi da mummunar ragargajewa kuwa.”
And the rain descended, and the floods came, and the winds blew, and beat upon that house; and it fell: and great was its fall.
28 Sa’ad da Yesu ya gama faɗin waɗannan abubuwa, sai taron mutanen suka yi mamakin koyarwarsa,
And it came to pass, when Jesus had ended these sayings, the people were astonished at his doctrine:
29 domin ya koyar kamar wani wanda yake da iko, ba kamar malamansu na dokoki ba.
For he taught them as one having authority, and not as the scribes.

< Mattiyu 7 >